Me ya sa Atiku ya dage kan dawo da tallafin man fetur?

Asalin hoton, Atiku Abubakar
Batun cire tallafin man fetur na ci gaba da haifar da muhawara a Najeriya gabanin babban zaɓen ƙasar na 2027.
Babban ɗan takara na hamayya, Atiku Abubakar ne ya tayar da ƙurar lokacin da ya sanar cewa zai mayar da tallafin man fetur idan ya lashe zaɓen ƙasar na 2027.
Kalaman na tsohon mataimakin shugaban ƙasar a makon da ya gabata sun ƙara zafafa siyasar ƙasar, lamarin da ya kai ga shugaban Najeriya Bola Tinubu da kansa ya fito ya soki lamirin kalaman na Atiku.
Sai dai a wani kalami da mai taimaka wa Atiku Abubakar kan yaɗa labarai, Kenneth Okonkwo ya yi a hirarsa da wata kafar talabijin ya nuna cewa kamar akwai sassauci kan batun janye tallafi, sai dai Atiku ya yi watsi da kalaman na Okonkwo.
A lokacin da ya ya yi bayani a gidansa da ke Abuja ranar Talata, Atiku ya sake nanata alwashin nasa.
"Zan nanata ɓaro-ɓaro cewa batun dawo da tallafin man fetur da na ce zan yi babu fashi", a cewar Atikun.
Ya ƙara da cewa "cire tallafin man fetur ya jefa mutane cikin talauci fiye da kowane lokaci a tarihin wannan ƙasa".
To sai dai a ƙoƙarin yin ƙarin haske game da bayanin na Atiku, na kusa da tsohon mataimakin shugaban ƙasar sun riƙa yin wasu kalamai da suka nuna shakku kan batun dawo da tallafin.
Daga cikin irin waɗannan mutane har da mai mara masa baya a takarar 2027 Rotimi Amaechi, da mai taimaka masa kan yada labari Paul Ibe da kuma wani mai taimaka masa kan yaɗa labaran Kenneth Okonkwo.
A lokacin taron ƙungiyar lauyoyi ta Najeriya (NBA) a birnin Fatakwal, Rotimi Amaechi, ɗan takarar mataimakin shugaban ƙasa na jam'iyyar ADC ya ce "Abin da Atiku Abubakar ke nufi ba shi ne kauce wa cire tallafin man fetur ba ko a'a, abin da muke son yi shi ne mu samar da ɗanyen man fetur cikin rahusa ta yadda za a tace a sayar a cikin farashi mai sauƙi ga al'umma'', in ji shi.
Za mu ci gaba da sabunta muku wannan labari...









