Mario Gotze zai bar Borussia Dortmund idan an kammala kakar 2019-20

Asalin hoton, Getty Images
An wallafa
Mario Gotze zai bar Borussia Dortmund da an kammala kakar bana in ji daraktan wasannin kungiyar Michael Zorc.
Mai shekara 27 ya buga wasa 201 a kaka biyu da ya yi a kungiyar, sai dai kuma karawa biyar ya yi wa Dortmund a kakar shekarar nan.
Gotze ya lashe kofin Bundesliga biyar, kuma shi ne ya ci wa Jamus kwallo a wasan karshe da ta lashe kofin duniya a 2014.
An yanke wannan shawarar, bayan da kocin Dortmund, Lucien Favre ya ce ba shi da inda zai saka dan kwallon a lokacin wasa.
Gotze ya fara da zaman benci a karawar da Dortmund ta doke Wolfsburg 2-0 a wasan mako na 27 ba tare da 'yan kallo ba.






