KAI TSAYE, Yaƙin Iran, Amurka da Isra'ila da sauran abubuwan da ke faruwa a sassan duniya ta ranar Talata 20/5/2026.

Wannan shafi ne da ke kawo muku labaran yaƙin Iran da sauran abubuwan da ke faruwa a sauran sassan duniya ta ranar Laraba 20 ga watan Mayun 2026.

  • Sadis Buba
  • Pantami
  • xxx
  • Nafiu Gombe
  • Mace da ƴarta mai lalaurar Autism
  • wata mata
  • BBC reporter

Rahoto kai-tsaye

Daga Aisha Babangida, Usman Minjibir da Nabeela Uba

  1. Amurka za ta sha mamaki idan ta koma yaƙi da mu - Iran

    ...

    Asalin hoton, EPA/Shutterstock

    Ministan harkokin wajen Iran, Abbas Araghchi, ya mayar da martani ga kalaman barazanar shugaban Amurka, Donald Trump, dangane da yiwuwar sake kai hari kan Iran, inda ya ce: “Amurka za ta sha mamaki idan ta koma fagen yaƙi da mu.”

    Araghchi ya yi wannan gargaɗi ne a wani sabon saƙo da ya wallafa a shafin X inda ya ce

    “Watanni bayan fara yaƙin da aka yi da Iran, Majalisar Dokokin Amurka ta amince da lalata jirage masu yawa da darajarsu ta kai biliyoyin daloli. Yanzu kuma an tabbatar a hukumance cewa rundunar sojinmu mai ƙarfi ita ce ta farko a duniya da ta harbo shahararren jirgin yaƙin F-35 ta Amurka.”

    A ƙarshen saƙon nasa, ya yi iƙirarin cewa:

    “Da darussan da muka koya da kuma ilimin da muka samu, ku tabbatar cewa komawa fagen yaƙi zai kawo ƙarin abubuwan mamaki.”

    A jiya ne shugaban Amurka, Donald Trump, ya yi iƙirarin cewa a daidai lokacin da ake shirin kai wani babban harin soji kan Iran, ya bayar da umarnin dakatar da harin bayan roƙon shugabannin yankin.

  2. Jiragen man China sun ratsa ta mashigar Hormuz bayan jinkirin fiye da wata biyu

    ....

    Asalin hoton, Getty Images

    Wasu manyan jiragen dakon mai guda biyu na ƙasar China da ke ɗauke da ganga miliyan huɗu na ɗanyen mai sun ratsa ta mashigar Hormuz a ranar Laraba.

    Bayanan jigilar ruwa daga kamfanonin Kepler da LSGA sun nuna cewa manyan tankokin man guda biyun da ke ɗauke da ɗanyen man Gabas ta Tsakiya sun bar mashigar Hormuz bayan sun shafe sama da wata biyu suna jira a yankin Tekun Fasha.

    A cikin kwanakin baya-bayan nan, jiragen ruwa kaɗan ne kawai suka rika bi ta wannan muhimmiyar hanyar ruwa.

    Sai dai nasarar da jiragen suka samu wajen wucewa, tare da sauyin salon magana daga Fadar White House, ya sa farashin mai ya ɗan sauka kaɗan.

    A ranar Talata, shugaban Amurka, Donald Trump, ya jaddada cewa ana dab da cimma yarjejeniyar zaman lafiya da Iran, duk da cewa ya ce duk wata yarjejeniya da za a cimma dole ne ta hana Iran mallakar makamin nukiliya.

  3. Assalamu alaikum

    Jama'a barkanmu da wannan safiya ta Laraba daga wannan shafin namu na BBC Hausa, inda za mu ci gaba da kawo muku labaran kai-tsaye na abubuwan da suke faruwa a Najeriya da sassan duniya.

    Za ku iya leƙawa shafukanmu na sada zumunta na facebook da X da kuma whatsapp domin karanta wasu labaran da kallon bidiyo da ma tafka muhawara.

    Ku kasance tare da mu.