Ghana ta kwashe ƴan ƙasarta kusan 800 daga Afirka ta Kudu

Asalin hoton, Reuters
Jami'ai daga Ghana sun mayar da kusan 'yan ƙasar 800 zuwa gida daga Afirka ta Kudu.
Hakan ya biyo bayan zanga zangar nuna ƙyama ga baƙin hauren da ake a wasu sassan biranen Afirka ta Kudu fiye da wata guda ke nan.
Wakiliyar BBC ta ce ta ga yadda gwamman mutane ke fita daga motocin bas inda suka isa filin jirgin saman Tambo suna hawa jirgin zuwa Accra.
Jakadan Ghana a Afirka ta Kudu ya ce gwamnatinsu na son tabbatar da cewa 'yan Ƙasarsu sun kuƁuta daga hare-haren da ake kai wa baƘin hauren.
Ghana ta ce tana tabbatar da tsare lafiyar 'yan Ƙasarta.
WaƊanda suke zanga zangar sun ce yawancin mutanen da ke shiga cikin Ƙasar ta Afirka ta Kudu ba bisa Ƙa'ida ba na mamaye musu guraben aiki a ma'aikatun gwamnati.








