KAI TSAYE, Yaƙin Iran da abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya 25/053/2026

Wannan shafi ne da ke kawo muku bayanai kan yaƙin Iran da kuma abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya na ranar Litinin 25 ga watan Mayun 2026

  • Sadis Buba
  • Pantami
  • xxx
  • Nafiu Gombe
  • Mace da ƴarta mai lalaurar Autism
  • wata mata
  • BBC reporter

Rahoto kai-tsaye

Daga Aisha Babangida da Haruna Kakangi

  1. An kashe sojan Isra'ila a Kudancin Lebanon

    ...

    Asalin hoton, Getty Images

    Sojojin Isra’ila sun ce an kashe wani sojansu yayin fafatawa a kudancin Lebanon.

    Isra’ilar ta kuma sanar da cewa wasu sojojin sun samu munanan raunuka inda aka kai su asibiti domin samun kulawar likita.

    Sai dai har yanzu ba a bayyana cikakkun bayanai kan yadda aka kashe sojan ko kuma inda arangamar ta faru ba.

  2. Farashin mai ya faɗi saboda fatan cimma yarjejeniya tsakanin Iran da Amurka

    ....

    Asalin hoton, Reuters

    Farashin ɗanyen mai ya faɗi sosai yayin da kasuwannin hannayen jari na Asiya suka samu ƙaruwa, sakamakon fatan cimma yarjejeniyar da za ta kawo ƙarshen yaƙin Iran.

    Shugaban Amurka, Donald Trump, ya ce a ranar Asabar ana ci gaba da tattaunawa sosai kan yarjejeniya da Tehran, yana mai cewa za a bayyana cikakkun bayanai nan ba da jimawa ba.

    Sai dai washegari ya gargaɗi tawagar masu tattaunawarsa da kada su yi gaggawar cimma yarjejeniya.

    A safiyar Litinin a kasuwannin Asiya, farashin ɗanyen man Brent ya sauka da kashi biyar cikin ɗari zuwa dala 98.36 kan ganga guda, yayin da ɗanyen man Amurka ya ragu da kashi 3.5 cikin ɗari zuwa dala 91.50 kan ganga.

    Trump ya taɓa cewa yarjejeniyar za ta haɗa da sake buɗe mashigar Hormuz, amma bai bayyana ƙarin bayani ba.

    Mashigin ruwan, wanda ake bi wajen jigilar kusan kashi ɗaya cikin biyar na man duniya da iskar gas ya kusa daina aiki tun bayan fara faɗan a ranar 28 ga Fabrairu.

  3. Majalisar Iran ta fara zamanta na farko tun bayan fara yaƙi

    ....

    Asalin hoton, Getty Images

    Majalisar dokokin Iran ta fara zamanta tun bayan fara yaƙi, inda ’yan majalisar suka halarci zaman a zauren majalisa karo na farko cikin fiye da kwanaki 80.

    Kafofin yaɗa labaran Iran sun ce an gudanar da zaɓen shugabancin majalisar ne a yayin zaman.

    Tun bayan fara yaƙin Isra’ila da Amurka da Iran ne aka dakatar da zaman majalisar, inda aka gudanar da zama guda ɗaya kacal ta hanyar intanet

  4. Assalamu alaikum

    Jama'a barkanmu da wannan safiya ta Litinin daga wannan shafin namu na BBC Hausa, inda za mu ci gaba da kawo muku labaran kai-tsaye na abubuwan da suke faruwa a Najeriya da sassan duniya.

    Aisha Babangida ke fatan kasancewa da ku a daidai wannan lokaci.

    Za ku iya leƙawa shafukanmu na sada zumunta na facebook da X da kuma whatsapp domin karanta wasu labaran da kallon bidiyo da ma tafka muhawara.

    Ku kasance tare da mu.