An sake buɗe masallacin Al-Aqsa da saura wuraren bauta a Birnin Kudus

Asalin hoton, Getty Images
‘Yan sandan Isra’ila sun sanar cewa za a sake buɗe wuraren ibada a Birnin Kudus ga masu ziyara da masu ibada bayan cimma tsagaita wuta na wucin gadi a rikicin Gabas ta Tsakiya.
Waɗannan wurare sun haɗa da Masallacin Al-Aqsa da Western Wall, da Cocin Holy Sepulchre a Tsohuwar Birni, wadanda suke daga cikin wuraren ibada mafi muhimmanci ga Musulmai da Yahudawa da Kiristoci.
Sakamakon yaƙin da Iran ke yi da Amurka da Isra’ilan ne aka rufe wadannan wurare.
Birnin Kudus ta kasance wurin da kullum cike take da mazauna, masu sayayya a kasuwa da masu yawon bude ido, da masu ibada.
‘Yan sanda sun ce za a buɗe wuraren ne a safiyar Alhamis, kuma za a tura ƙarin ‘yan tsaro da dama don tabbatar da tsaro.







