Ban taɓa haɗuwa da Adeyemi ba — Gbajabiamila
Shugaban ma’aikatan fadar shugaban Najeriya, Femi Gbajabiamila, ya musanta cewa ya taɓa haɗuwa ko yin wata mu’amala da Adeniyi Adeyemi, wanda ya bayyana kansa a matsayin Darakta Janar na hukumar PFIPC.
Adeyemi wanda gwamnatin tarayyar ƙasar ta ce ya naɗa kansa a matsayin shugaban majalisar bai wa shugaban shawara kan tattalin arziki da zuba jari daga ƙasashen ƙetare, ya zargi Gbajabiamila da yin barazana ga rayuwarsa bayan turka-turka ta ɓarke tsakaninsu.
Sai dai Gbajabiamila ya ce ba shi da wata alaƙa ko mu’amala da Adeyemi a baya.
A cikin wata wasiƙa da lauyansa, Kemi Pinheiro ya aika wa Adeyemi a madadinsa, Gbajabiamila ya buƙaci Adeyemi ya janye kalamansa tare da neman afuwarsa a gidajen jaridu biyar na ƙasar da kuma shafukan sada zumunta da aka yaɗa zarge-zargen.
"Wanda mu ke wakilta [Gbajabiamila] ya shaida mana cewa, ba ka taɓa haɗuwa da shi ba, ba ka taɓa yin wata mu’amala, ko wata hulɗa ta sirri ko aiki da shi ba,” in ji Lauyan.
A cikin wasiƙar, lauyoyin Gbajabiamila sun ce idan Adeyemi bai cika waɗannan buƙatu cikin sa’o’i 72 ba, za su ɗauki matakin shari’a a kansa, ciki har da shigar da ƙara kan zargin ɓata suna.
Sun ce za su kuma nemi diyyar Naira biliyan 10, tare da umarnin kotu da zai tilasta masa bayar da haƙuri da kuma dakatar da sake yaɗa irin waɗannan zarge-zarge.
Wannan rikici ya samo asali ne daga zarge-zargen da Adeyemi ya yi a wani taron manema labarai da ya gudanar a watan da ya gabata, inda ya yi ikirarin cewa Gbajabiamila na da hannu wajen tafiyar da harkokin PFIPC.