Nicaragua ta soke lasisin lauyoyi 2,000
Hukumomi a Nicaragua sun soke lasisin lauyoyi 2,000 ba tare da bayyana dalilin yin hakan ba.
Kafafen yaɗa labarai na Nicaragua sun ruwaito cewa an cire sunayen lauyoyin daga rajistar Kotun Koli, matakin da ya hana su ci gaba da gudanar da aikinsu na lauya.
Majalisar Ɗinkin Duniya ta ce wannan mataki zai rufe hanya ta ƙarshe da ta rage ga mutanen da ke neman kariyar shari'a daga gwamnatin da ake zargi da mulkin kama-karya ƙarƙashin Daniel Ortega da matarsa, Rosario Murillo.
Ma'auratan sun shafe kusan shekara 20 suna mulkin Nicaragua da cikakken iko, tare da riƙe madafun iko