An yi wa Polio taron-dangi a Afirka

Polio
Bayanan hoto, Ana yi wa yara muliyan 100 'yan kasa da shekaru biyar rigakafin Shan Inna
An wallafa

An kaddamar da wani gagarumin aikin rigakafin cutar Shan Inna wato Polio a Najeriya da wasu sassa na Afirka.

Ma'aikatan kiwon lafiya za su yi wa yara fiye da muliyan 100 rigakafi a Yammaci da Taskiyar Afirka a wani yunkuri na shawo kan bazuwar cutar bayan da aka samu barkewarta a arewa maso gabashin Najeriya mai fama da bala'in rikicin Boko Haram.

A Najeriya dai ma'aikatan rigakafin za su bi gida-gida, da masallatai da majami'u da kasuwanni da sauran wurare da za a iya samun yara da ba su wuce shekara biyar da haihuwa ba.

Jami'an Shirin Kawar da Cutar Polio a Duniya na cewa za a yi aikin rigakafin a kasashe goma sha uku a nahiyar Afirka. Za a yi kwanaki hudu ana aikin rigakafin.

Bayan da aka yi tsammanin an kawar da cutar ta Shan Inna a Afirka inda aka yi shekaru biyu ba a samu yaron da ya kamu da kwayar cutar ba , sai kwatsam aka bada labarin sake bullarta a Najeriya a bara.

Yara hudu ne aka samu suna dauke da kwayar cutar a jihar Borno dake arewa maso gabashin kasar.

To sai dai tun daga lokacin aka fara yunkurin rigakafi zagaye-zagye, kuma wannan shi ne zagaye na karshe wanda ya hada kasashen Afirka da dama.

Kwamishinan lafiya a jihar ta Borno, Dokta Haruna Mshelia, ya shaida wa Ishaq Khalid ta wayar tarho cewa aikin yana gudana yadda aka tsara.

Saurari karin bayani a hirarsu:

Bayanan sautiPolio na nakasa kananan yara a duniya a cewar WHO

Ayyukan tarzoma na Boko Haram sun tarwatsa dimbin mutane, abinda ya haifar da fargabar cewa cutar za ta iya yaduwa zuwa makwabtan kasashe da ma nahiyar baki daya.

A duniya baki daya, kasashe uku ne ake da cutar a halin yanzu, wato kasashen Najeriya da Afghanistan da Pakistan a cewar Hukumar Lafiya ta Duniya, WHO.