KAI TSAYE, Abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya 02/07/2026

Wannan shafi ne da ke kawo muku labaran abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya

Skip Bidiyo and continue reading
  • Zanga-zanga a aAfirka ta Kudu
  • xxx
  • Ummulkhairi Aliyu
  • xxx
  • xxx
  • xxx
  • xxx
  • Arsenal
  • xxx
  • xxx
  • xxx
  • xxx
  • Kutama
  • xxx

Rahoto kai-tsaye

Ibrahim Yusuf Mohammed

  1. Trump ya ce tattaunawa da Iran na tafiya yadda ya kamata.

    ...

    Asalin hoton, Getty Images

    Shugaban Amurka Donald Trump ya bayyana a ranar Laraba cewa al'amura na tafiya yadda ya kamata a tattaunawar da ake yi da Iran, kuma an samu matuƙar ci gaba a tarukan da aka yi a Qatar a cikin kwanakin nan.

    "Tsarin wargaza shirin nukiliyar Iran yana tafiya yadda ya kamata. Sun gudanar da tarurruka masu kyau," in ji Mista Trump ga manema labarai kafin ya tafi North Dakota.

    Iran ta ci gaba da jaddada yanayin zaman lafiya na shirin nukiliyarta.

    Donald Trump ya kuma ce: "Mun matsa musu matuƙa... amma muna da kyakkyawar fahimta da juna."

    Ana gudanar da tattaunawar da ba na kai-tsaye ba tsakanin Iran da Amurka a yau a Doha, wanda Qatar da Pakistan ke shiga tsakani.

  2. 'An ƙona gomman mutane da ransu a rikicin jihar Neja'

    ...

    Asalin hoton, @HonBago

    Ƴan sanda sun bayyana cewa, an kashe aƘalla mutum 18 a jihar Neja, dake yankin Arewa ta tsakiyar Najeriya, sakamakon jerin hare-haren da ke da nasaba da dogon rikici tsakanin manoma da makiyaya.

    Kakakin rundunar ƴan sandan jihar, Wasiu Abiodun, ya ce jami’ai sun samu rahoto daga yankin Katako na ƙaramar hukumar Rafi cewa wasu ƴan bindiga sun kai hari ƙauyen Godoro a daren ranar Litinin.

    Ya ce an harbe wani matashi mai shekara 25 har lahira, lamarin da ya sa mambobin ƙungiyar sa-kai ta yankin suka tare hanya tare da kashe wani mutum mai shekaru 28 a matsayin ramuwar gayya.

    Ƴan sanda sun ce a wani lamari na daban a ranar Talata da daddare, an kona mutane 15 har lahira a wani gida mai ɗakuna biyu a Angwan-Baago kusa da ƙauyen Godoro, yayin da aka kashe wani mutum a wani wuri na daban, wanda ya kawo adadin mace-macen da aka tabbatar ya kai aƙalla 18.

    Duk da haka, majiyoyin yankin sun ce jimillar waɗanda suka mutu na iya kai wa 48 bayan jerin hare-hare da ramuwar gayya.

    Wani mazaunin yankin, Hamza Maisaje Kwana, ya ce "Ko da yake ba za mu iya tabbatar da ainihin adadin waɗanda abin ya shafa ba, kiyasinmu ya nuna cewa an kashe mutane 43," in ji shi.

    Ƴansakai ƙungiya ce wadda galibi ta kunshi Hausawa manoma a arewacin Najeriya.

    An kafa su ne a yankin don kare al'ummomi daga Ƴan fashin daji.

    Duk da haka, an kuma zarge su da aikata kisan kai da cin zarafi ga makiyaya Fulani ba bisa ƙa'ida ba.

    A na su ɓangaren kuma wasu Fulani makiyaya sun kafa nasu ƙungiyoyin.

    Tashe-tashen hankula makamantan wannan sun ja hankalin ƙasashen duniya a cikin ƴan shekarun nan, inda al'ummomi daban-daban ke zargin juna da kai hare-hare.

    An kashe dubban mutane a cikin shekaru da dama na rikice-rikicen ƙabila da addini masu sarƙaƙiya, galibi sun samo asali ne daga taƙaddama kan amfani da filaye tsakanin al'ummomin da galibi ke noma da kuma ƙungiyoyin makiyaya.

  3. Wani babban jami'in gwamnatin China zai halarci jana'izar Ali Khamenei.

    ...

    Asalin hoton, Getty Images

    Ma'aikatar harkokin wajen ƙasar China ta sanar a ranar Alhamis cewa, babban jakadan ƙasar He Wei, zai je Tehran domin halartar jana'izar tsohon shugaban Iran, Ali Khamenei.

    Shi ne mataimakin shugaban kwamitin dindindin na majalisar wakilan Jama'ar ƙasa, wato babbar majalisar dokoki ta ƙasar China.

    An kashe Ali Khamenei tare da wasu daga cikin ƴan uwansa a ranar farko ta harin da Amurka da Isra'ila suka kai kan Iran a ranar 21 ga watan Maris, 2026.

    An tsara gudanar da jana'izar Khamenei ne cikin kwanaki biyar.

    Dangane da shirye-shiryen da aka sanar, za a fara gudanar da jana'izar ne a ranar Asabar, 4 ga watan Yuli a birnin Tehran, sannan zai kammala a ranar 8 ga watan Yuli tare da binne Ali Khamenei a birnin Mashhad.

  4. Amurka da dawo da jigilar daloli zuwa Iraƙi

    ...

    Asalin hoton, Getty Images

    Jaridar New York Times ta ruwaito a ranar Alhamis, cewa Amurka ta ci gaba jigilar daloli zuwa Iraki bayan dakatar da ayyukanta na watanni da dama.

    Jaridar dia ta alaƙanta bayanan da wasu mataimakan firaministan Iraƙi guda biyu.

    "An sake komawa aikin jigilar dalar Amurka zuwa Iraƙi," in ji Haider al-Abboudi, ɗaya daga cikin masu magana da yawun Firaministan Iraki, yayin da yake zantawa da jaridar.

    A cewar wannan rahoto, Mudhar Muhammad Saleh, mai bai wa Firaministan Iraƙi shawara kan harkokin kuɗi, shi ma ya tabbatar da hakan.

    A watan Afrilu, Amurka ta dakatar da jigilar kuɗin da suka kai dala miliyan 500 zuwa ƙasar,

    sannan ta dakatar da wasu daga cikin ayyukan haɗin gwiwar tsaro da ta ke yi da Baghdad.

    Manufar wannan mataki ita ce matsa wa gwamnatin Iraƙi lamba domin ta hana ayyukan ƙungiyoyin mayaƙa da Iran ke marawa baya a ƙasar.

  5. An yi wa karnuka aƙalla 400 kisan gilla

    xxx

    Asalin hoton, UGC

    Mazauna garin Hossana, a yankin Tsakiyar Habasha, sun ba da rahoton cewa an kashe ɗaruruwan karnuka bayan jerin hare-haren cizon kare da suka yi sanadiyyar mutuwar wasu mutane a yankin.

    Mazauna da jami'ai sun ce kisan ya fara ne bayan mutuwar wasu yara uku sakamakon matsalolin da suka shafi cutar haukar karnuka.

    A cewar shaidun gani da ido, wakilan unguwa sun umurci mazauna yankin da su kashe karnukansu ba tare da la'akari da matsayinsu na rigakafi ba.

    An ruwaito cewa an tilasta wa masu gidaje su shake dabbobinsu da igiya ko kuma su lakaɗa musu duka har sai sun mutu.

    Waɗanda suka ƙi bin umarnin sun fuskanci tarar da ta kai dalar amurka 300.

    Wani mazaunin yankin ya shaida wa BBC ba tare da an ambaci sunansa ba cewa kisan ya fara ne bayan da wasu ƴan'uwa biyu suka mutu sakamakon cizon karnuka. "Duk da cewa an yi allurar riga-kafi, wakilan unguwa sun fara aikin kashe dukkan karnuka ba tare da la'akari da yanayin lafiyarsu ba, ko an yi musu allurar riga-kafi ko a'a.

    Wani shaida mai suna Alaazar Kebede, wanda likitan dabbobi ne, ya shaida wa BBC cewa, "Duk da cewa an riga an yi allurar rigakafi, wakilan unguwa sun fara yaƙin neman kawar da duk karnukan yankin. An umurci masu karnukan da su kashe dabbobinsu, kuma an kama waɗanda suka ƙi yin hakan. Muna hasashen cewa an kashe karnuka tsakanin 400 zuwa 450 a cikin 'kan kwanaki kaɗan."

    "Alaazar ya ƙara da cewa, "Mutane suna jan karnuka suna kashe su ta munanan hanyoyi. Wannan rashin ɗa'a ne kuma ba a yarda da shi ba a addinance, da al'adance, da kuma a fuskar doka.''

    Bidiyo ya nuna yadda masu karnukan ke ta sharɓa kuka yayin da ake kashe karnukansu.

  6. BBC ta gano wani mai safarar mutane da aka yanke wa hukunci a Faransa yana zaune a Birtaniya

    ...

    Wani bincike na BBC ya gano wani mai safarar mutane da aka yanke wa hukunci, wanda a da aka yi wa laƙabi da "ubangidan" sansanonin ƴan ci-rani na Faransa, yana zaune a Leicestershire kuma ana kyautata zaton yana neman mafaka yayin da yake aiki ba bisa ƙa'ida ba.

    An yanke wa Twana Jamal hukuncin ɗaurin shekara biyar a gidan yari a Faransa a shekarar 2016, inda hukumomi suka bayyana shi a matsayin ɗaya daga cikin manyan masu safarar mutane da aka taba kamawa.

    Masu gabatar da ƙara sun ce ɗan Iraƙin, mai shekara 36 a lokacin, ya samu har zuwa £100,000 a mako guda saboda jigilar bakin haure ba bisa ƙa'ida ba zuwa ƙasashen Turai.

    Bayan samun wasu bayanai a kansa a cikin wannan shekarar, mun gano Jamal a ƙauyen Blaby kuma mun samu shaida yana aiki, yana tuƙa mota ba tare da lasisi ba kuma da alama yana amfani da sunan ƙarya.

    Kasancewar Jamal a Burtaniya ta haifar da damuwa sosai game da ko hukumomin kan iyaka da ke akwai suna da tasiri wajen gano masu neman mafaka waɗanda suka aikata manyan laifuka a ƙasashen waje.

  7. Aƙalla mutum 18 sun mutu bayan harin da Rasha ta ƙai babban birnin Ukraine

    ...

    Asalin hoton, Reuters

    Jami'ai sun ce dakarun Rasha sun kai wani mummunan harin makami mai linzami a babban birnin Ukraine Kyiv cikin dare, inda suka kashe aƙalla mutum 18.

    An kwashe mutane da dama daga gidajensu yayin da hare-haren suka girgiza gine-gine a faɗin birnin, sa'o'i bayan da shugaban Ukraine Volodymyr Zelensky ya yi gargaɗin cewa Rasha na shirin kai wani babban hari.

    Rahotanni na cewa yara na cikin akasarin waɗanda suka mutu, in ji Tymur Tkachenko, shugaban gwamnatin soji ta Kyiv.

    "Maƙiyan mu suna sake kai hari kan ungwannin mutane da gangan suna kashe fararen hula," in ji shi da sanyin safiyar Alhamis.

    Ma'aikatar Tsaro ta Rasha ta yi iƙirarin cewa ta kai hari kan cibiyoyin makamashi ne saboda hare-haren da Ukraine ta kai kwanan nan.

  8. Assalamu Alaikum!

    Jama'a barkanmu da wannan safiya ta Alhamis daga wannan shafin namu na BBC Hausa, inda muke kawo muku labaran kai-tsaye na abubuwan da suke faruwa a Najeriya da sassan duniya.

    Za ku iya leƙawa shafukanmu na sada zumunta na facebook da X da kuma whatsapp domin karanta wasu labaran da kallon bidiyo da ma tafka muhawara.

    Ku kasance tare da mu.