Yaƙin Iran da Amurka da Isra'ila da kuma abubuwan da ke faruwa a Najeriya 30/03/2026

Wannan shafi ne da ke kawo muku rahoto kan yaƙin Iran da Amurka da Isra'ila da kuma abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya na ranar Litinin 30 ga watan Maris 2026.

Rahoto kai-tsaye

Daga Aisha Babangida da Haruna Kakangi

  1. Trump ya ce yana son mallake man ƙasar Iran

    ..

    Asalin hoton, Getty Images

    Shugaba Trump na Amurka ya ce yana son mallake man Iran, kuma mai yuwuwa ya ƙwace tsibirin Kharg - inda yawanci Iran take samun man da take fitarwa waje.

    Shugaban yana magana ne da jaridar Financial Times, yayin da dubban sojojin ƙundumbala na Amurka ke kan hanyarsu ta zuwa yankin na Gabas ta Tsakiya.

    Wakilin BBC ya ce, da yake magana a cikin jirgin shugaban ƙasa - AirForce One a daren da ya gabata - Trump ya ce Iran a shirye take ta miƙa tsibirin, in ba haka ba zai zama ba ta da wata sauran ƙasa kuma.

    Sai dai kuma daga baya Trump din ya ce za a iya cimma matsaya da Iran, yana mai bayyana jagororin ƙasar da cewa suna yin abin da ya dace.

    Yaƙin na Iran ya sa farashin mai a duniya na ta tashi, inda a yanzu haka ɗanyen man samfurin Brent ya sake tashi zuwa kusan dala 116 kan kowace ganga.

  2. Yadda Sanata Rabi'u Musa Kwankwaso ya sauya sheƙa zuwa ADC

    Bayanan bidiyo, Yadda sanata Rabi'u Musa kwankwaso ya sauya sheƙa zuwa ADC
  3. Australia za ta kashe dala biliyan biyu wajen tallafa wa ƴan ƙasa

    ..

    Asalin hoton, Getty Images

    Majalisar zartarwa ta Australia ta amince da shirin da gwamnatin ƙasar ta ɓullo da shi na sauƙaƙa wa jama'a da tallafin mai - wanda za ta kashe dala biliyan biyu da rabi.

    Firaminista Anthony Albanese ya ce gwamnati za ta rage rabin kuɗin fito a kan man fetur da man gas na dizil tsawon wata uku.

    Haka kuma ya buƙaci jama'a, da su riƙa amfani da ababan hawa na jama'a domin alkinta man don masana'antu da ke buƙatarsa.

    A wasu wuraren kusan farashin man dizil ya ninka biyu tun bayan da aka fara yaƙi a Gabas ta Tsakiya.

    Daga ranar Lahadi wasu jihohi biyu a ƙasar ta Australia sun ɓullo da shirin wucin-gadi na sauƙaƙa wa jama'a hawa motoci da sauran ababan hawa na jama'a kyauta.

  4. Jirgin dakon man Rasha ya isa Cuba

    ..

    Asalin hoton, Getty Images

    Ana sa ran wani jirgin dakon mai na Rasha, da ke ɗauke da dubban gangunan ɗanyen mai ya isa Cuba a wannan makon, bayan da Shugaba Trump na Amurka ya gaya wa 'yan jarida cewa, ba shi da wata matsala idan Rasha za ta aika wa ƙasar ta Cuba mai.

    Amurka dai ta sanya wa ƙasar ta Cuba takunkumin shigar mata da mai a watan Janairu, tare da barazana ga duk wata ƙasa da ta aika mata mai.

    Wakilin BBC ya ce, ba a dai sani ba ko kalaman na nufin sauyi ne na matakin gwamnatin Amurka na hana shigar mata da man ko kuma sauƙi ne na wucin- gadi.

    Cuba na fuskantar matsalar ƙarancin mai mafi muni wanda ba ta taɓa shiga irinta ba, tun bayan yaƙin cacar-baka, kusan saboda matakin da Amurka ta ɗauka na hana kai mata man.

  5. Spain ta rufe sararin samaniyarta ga jiragen yaƙin Amurka da suka kai wa Iran hari

    ..

    Asalin hoton, Getty Images

    Ministan tsaron ƙasar Sipaniya, Margarita Robles ta ce ƙasar ta rufe sararin samaniyyarta ga jiragen yaƙin Amurka da suka kai hare-hare kan Iran.

    "Ba za mu bari an yi amfani da sansanin sojin Moron and Rota domin aikata duk wani abu mai alaƙa da yaƙar Iran ba," in ji ta inda ta ƙara da cewa Sipaniya ta "fayyace wa gwamnatin Amurka matsayarta tunda fari."

    Ministan harkokin wajen ƙasar, Jose Manuel Albares ya ce manufar ɗaukar matakin ita ce "ka da a yi duk wani abun da zai iya rura wutar yaƙin."

    Wani jami'an fadar White House ta Amurka ya shaida wa BBC cewa sojojin Amurka na "samun nasara ko ma sun wuce nasarar da ake son cimma a yakin saboda haka Amurka ba ta buƙatar taimakon Sipaniya ko waninta."

    A baya dai Donald Trump ya yi barazanar ƙaƙaba wa Sipaniya takunkumi bisa ƙin adawar da take da yaƙar Iran.

  6. Yadda ginin wani coci ya ruguzo a Ghana

    ..

    Asalin hoton, Getty Images

    Ginin wani coci ya ruguje a babban birnin Ghana, Accra inda ya kashe aƙalla mutum biyu, wasu da dama kuma suka maƙale cikin ɓaraguzai.

    Ba a dai san mutum nawa ne a ciki a lokacin da suke ibada ba, amma dai an ceci mutum 14, sai dai waɗanda ke wajen sun ce suna iya jin muryar mutane daga cikin ɓuraguzai.

    Masu aikin ceto a cikin daren da ya gabata na ta fama don gano wadanda buraguzan suka binne.

    An ce ginin mai hawa uku na wata tsohuwar makaranta ne aka mayar da shi coci na wucin-gadi .

    Ya kuma ruguje ne bayan wani mamakon ruwan sama da aka yi a babban birnin na Ghana.

  7. Su wane ne ƴan wasan gaba da suka fi ƙwazo da zura ƙwallo a tarihi?

    ..

    Asalin hoton, BBC Sport

    Za a iya cewa tun yana shekara 18, gwarzon ɗan kwallon Brazil, Ronaldo ya shiga jerin ƴan wasan gaba da ake ji da su.

    A lokacin yana zura ƙwallaye kamar ruwa a ƙungiyar PSV, ga kuma yanka a kafarsa da kuma salon burgewa wajen cin kwallo, abin da ya haska shi har ya koma Barcelona da kuma Inter Milan kafin shekara 21.

    A matsayinsa na matashin da ya taɓa lashe kyautar gwarzon ɗan kwallon duniya Ballon d'Or bayan zura kwallaye 200 ga ƙungiya da kuma ƙasarsa, Ronaldo mai shekara 23 ya nuna cewa zai mamaye ɓangaren kwallon kafa - idan ba gwiwarsa da ta kawo masa cikas ba a watan Afrilun, 2000.

    Duk da haka, hakan baya nufin cewa tauraruwarsa ta dakushe a lokacin, sai dai raunin ya buɗe kofa ga wasu su ma su haska - shin wane ne ɗan wasan gaba mafi hazaƙa a ƙarni na 21?

  8. Ko sulhun da Pantami ya yi wa El-Rufai da Uba Sani zai ɗore?

    ..

    Asalin hoton, Social Media

    Ƴan Najeriya na ci gaba da tafka muhawara musamman a shafukan sada zumunta game da sulhu da fitaccen malamin Addinin Musulunci Sheikh Ali Isa Pantami ya yi wa El-Rufai da Uba Sani.

    Al'amarin ya ɗauki hankalin mutane da dama musamman waɗanda ke bibiyar abubuwan da suka shiga tsakanin tsohon gwamna da gwamnan jihar na yanzu.

    Mutanen biyu dai sun jima ba sa ga maciji da juna, sakamakon rashin jituwa da ta shiga tsakaninsu, jim kaɗan bayan saukar El-Rufai daga mulkin jihar Kaduna.

    Malamin ya yi musu sulhu ne a lokacin jana'izar mahaifiyar El-Rufai, Hajiya Umma ranar Lahadi a Abuja.

    Jana'aizar ta samu halartar fitattun ƴansiyasar Najeriya, ciki har da waɗanda ke takun-saƙa da tsohon gwamnan.

  9. Ministan harkokin wajen Najeriya, Yusuf Tuggar ya ajiye aikinsa

    ..

    Ministan harkokin wajen Najeriya, Ambasada Yusuf Tuggar ya ajiye aikinsa na minista ranar Litinin.

    A wata takardar ajiye aiki da ya miƙa ga ofishin sakataren gwamnatin tarayya, Tuggar ya bayyana godiyarsa ga shugaba Bola Tinubu da ya ba shi dama.

    Duk da dai ambasada Tuggar bai faɗi dalilin ajiye aikin ba, amma bayanai na nuna ya ajiye aikin ne domin tsaya takarar gwamna a jihar Bauchi.

    Tuggar shi ne minista a gwamnati shugaba Tinubu da ya fara ajiye aikinsa domin tsayawa takara kafin cikar wa'adin da shugaba Tinubu ya ba su na ajiye mukamin gwamnati.

  10. Isra'ila ta ce mutum 6,000 ne suka jikkata sakamakon hare-haren Iran

    ..

    Asalin hoton, Getty Images

    Ma'aikatar Lafiyar Isra'ila ta ce kawo yanzu aalla mutum 6,000 ne aka kwantar da su a a asbiti sakamakon hare-haren Iran.

    Ma'aikatar ta ce har kawo yanzu akwai mutum 121 da ake kula da su a asibitoci, inda mutum aya yake cikin mummunan hali sannan 16 ke yanayin mutu kwakwai rai kwakwai.

    Ma'aikatar ta lafiya ta kuma ara da cewa an kai wasu ƙarin mutum 232 da suka jikkata zuwa asibitoci cikin dare.

  11. Nato ta ce ta kakkaɓo makaman linzamin Iran da suka nufi Turkiyya

    Kungiyar tsaro ta Nato ta ce makaman tsaron samaniyar ƙasashen ƙungiyar sun kakkaɓo makaman linzamin da Iran ta harba da suka nufi Turkiyya.

    Cikin wata sanarwa da kakakin ƙungiyar ya ce ya wallafa a shafinsa na sad zumunta ya ce ''Nato ta samu nasarar kakakɓo makaman linzamin Iran da suka yi yunƙurin shiga Turkiyya''.

    "NATO ta shirya wa wannan barazana, kuma a kodayaushe za ta duk abin da ya dace domin kare ƙawayenta.''

  12. Isa Ashiru Kudan ya fice daga PDP

    kkk

    Asalin hoton, Others

    Tsohon an takarar gwamnan jihar Kaduna na jam'iyyar PDP, Isa Ashiru Kudan ya fice daga jam'iyyar.

    Cikin wata sanarwa da ya fitar, Ashiru ya ce ya auki matakin ne sakamakon rigingimun da ya ce jam'iyyar na fama da su.

    Ashiru ne ya zo na biyu a zaɓen gwamnan jihar Kaduna na 2023.

    Ficewar ta sa na zuwa ne a daidai lokacin da siyasar Najeriya ta fara ɗaukar ɗumi.

    A baya-bayan nan jam'iyyar APC ta ADC na ci gaba da jan sabbin magiya baya, inda mutane daga jam'iyyu daban-dban ke komawa cikinsu.

  13. Mun kai wa na'urar tsaron samaniyar Iran hari - Isra'ila

    Sojojin Isra'ila sun ce sun kai hari cibiyar na'urorin tsaron samaniyar Iran da ke kusa da Tekun Caspian hari.

    Wurin an ɓoye shi cikin wani yanki mai surƙuƙin daji da ke da tazarar mil 1,000 daga Isra'ila, kamar yadda sojojin Isra'ilar suka bayyana cikin wata sanarwa da suka wallafa a shafinsu na X.

    Isra'ila ta ce wurin na zama barazana ga rundunar sojin saman Isra'ila da jiragenta.

  14. Iran na ci gaba da jerin hare-hare a yankin Gulf

    Iran na ci gaba da harba makamai masu linzami da jirage marasa matuƙa kan Isra'ila da kasashen Gulf.

    Gwamnatin Kuwait ta ce wani hari da aka kai a tashar samar da wutar lantarki da kuma masana'antar tsabtace ruwan sha ya kashe wani ma'aikacin Indiya guda.

    Sai dai rundunar sojin Iran ta musanta kai harin, inda ta ce Isra'ila ce ta kai shi.

    Rundunar tsaron Kuwait ɗin ta kuma ce ta kakkaɓo wasu jirage marasa matuƙa guda biyar.

    A gefe guda kuma ma'aikatar tsaron Saudiyya ta ce dakarunta sun sake kakkaɓo wasu makamai masu linzami guda biyar.

  15. Sojojin Isra’ila sun sake kai hari kan jami’ar Imam Hossein ta Iran

    Dakarun sojin Isra'ila IDF sun ce sun sake kai hari kan jami’ar Imam Hossein a cikin kwanakin nan.

    A cikin wata sanarwa da dakarun suka fitar, sun ce jami’ar na ɗauke da wasu muhimman wuraren rundunar juyin juya halin Iran inda ake gudanar da bincike da haɓaka makamai.

    Wannan na zuwa ne bayan wani irin hari da aka kai a baya kan harabar jami’ar a ranar 7 ga watan Maris, inda IDF ta bayyana cewa ita ce ta kai hari a wurin.

    Jami’ar tana cikin birnin Tehran kuma tana da alaƙa da rundunar juyin juya halin Iran.

  16. Kwankwaso ya koma jam'iyyar ADC tare da magoya bayansa

    ...

    Asalin hoton, Rabiu Kwankwaso/FB

    Tsohon gwamnan jihar Kano kuma jagoran Kwankwasiyya, Rabiu Musa Kwankwaso ya koma jam’iyyar haɗaka ta ADC tare da magoya bayansa bayan ficewarsa daga jam’iyyar NNPP.

    An gudanar da bikin komawarsa ne a gidansa da ke Kano, inda shuwagabannin jam’iyyar da dimbin magoya bayansa suka hallara domin tarbar sa.

    Tsohon gwamnan ya kuma buƙaci magoya bayansa su yi rajistar jamʼiyyar, tare da samun katin zaɓe na ƙasa.

    A jiya ne Kwankwaso ya sanar da ficewarsa daga NNPP, yana mai cewa matakin na daga cikin kokarin haɗa kai da wasu jam’iyyu domin kawo sauyi a ƙasar.

    Ya bayyana cewa lokaci ya yi da za a samar da hadin gwiwa tsakanin manyan ‘yan adawa, domin tinkarar kalubalen da Ƙasar ke fuskanta da kuma inganta shugabanci.

    Sai dai har yanzu ɓangaren NNPP ba su fitar da wata sanarwa mai karfi kan ficewar tasa ba.

  17. Trump ya sake nanata Amurka na tattaunawa ta gaskiya da Iran

    ....

    Asalin hoton, EPA

    Shugaban Amurka, Donald Trump ya sake cewa Amurka na tattaunawa ta gaskiya da Iran, wadda ka iya kai wa ga 'daukar matakin sojin idan har ba a cimma yarjejeniya ba'.

    A wani saƙo da ya wallafa a shafinsa na Truth Social, Trump ya bayyana Iran a matsayin “sabuwar gwamnati” ta Iran, wadda ya ce ta fi ta baya “yin tunani da hankali”.

    Trump ya ce an samu “gagarumin ci gaba”, amma ya kuma yi barazanar cewa “idan ba a cimma yarjejeniya nan kusa ba, ko kuma ba a buɗe mashigin Hormuz ga harkokin kasuwanci nan take ba,” Amurka za ta “lalata gaba daya” dukkan tashoshin wutar lantarki da tsibirin Kharg, da kuma wasu cibiyoyin tace ruwan tekun Iran.

    Ya jaddada cewa har yanzu Amurka ba ta lalata wadannan muhimman wurare “da gangan ba”.

    Trump ya kuma ce wannan mataki zai kasance martani ne ga “sojoji da sauran mutane da dama da Iran ta kashe a cikin shekaru 47 na mulkin tsohuwar gwamnatin da ya kira mai muni”.

    Sai dai ma’aikatar harkokin wajen Iran ta sake nanata cewa babu wata “tattaunawa kai tsaye” da ta gudana tsakanin Tehran da Washington tun bayan fara wannan rikici.

  18. Harin Iran ya haddasa gobara a matatar man Haifa da ke arewacin Isra'ila

    ....

    Asalin hoton, Reuters

    Wani sabon harin makami mai linzami da Iran ta kai ya haddasa gobara a wata matatar mai da ke Haifa a arewacin Isra’ila.

    Bidiyoyin da aka fitar sun nuna yadda wuta ta kama ɗaya daga cikin manyan tankunan matatar, inda kuma hayaƙi ya rika tashi sama.

    Kamfanin dillancin labarai na AP ya ruwaito cewa wannan ne karo na biyu da Iran ke kai hari kan matatar mai ta Haifa a yayin wannan rikici na baya-bayan nan.

    Rahotanni sun ce an samu nasarar shawo kan gobarar.

    Hukumar kashe gobara ta Isra’ila ta shaida wa Reuters cewa wani tankin ajiyar mai ya samu illa sakamakon harin.

    Isra’ila da na da matatun mai guda biyu ne.

  19. PDP tsagin Wike ta zaɓi sabbin shugabanninta

    ....

    Asalin hoton, PDP

    Jam'iyyar PDP tsagin Mininstan Abuja, Nyesom Wike ta zaɓi Abdulrahman Mohammed a matsayin sabon shugabanta na ƙasa yayin da Samuel Anyanwu ya samu matsayin sakataren jam'iyyar na ƙasa.

    Mohammed da Anyanwu sun samu kujerunsu ta hanyar masalaha, tare da sauran mambobin kwamitocin jam'iyyar ta ƙasa guda 19 a babban taron jam'iyyar na shekarar 2026 da aka gudanar a babban filin wasa na Moshood Abiola da ke Abuja a ranar Lahadi.

    Daga cikin manyan ‘yan jam’iyyar da suka halarci taron akwai tsohon gwamnan Jihar Jigawa, Sule Lamido da tsohon shugaban Majalisar Dattijai, Bukola Saraki da tsohon gwamnan Jihar Kaduna, Ahmed Makarfi, da sauransu.

    Wike, wanda aka bayyana a matsayin jagoran jam'iyyar ta ƙasa ya ce an fara warkar da PDP daga matsalolin da take fuskanta.

    Ya tabbatar wa mambobi cewa PDP za ta shiga zaɓe a shekarar 2027.

  20. Abin da muka sani kan kashe-kashe a Jos

    ....

    Asalin hoton, X/Caleb Mutfwang

    Gwamnatin jihar Filato ta ayyana dokar hana zirga-zirga ta awa kwana biyu a ƙaramar hukumar Jos ta Arewa bayan wani mummunan hari a ranar Lahadi, wanda bayanai suka ce ya yi sanadiyyar rayukan mutane da dama.

    Haka nan an samu mutane da yawa waɗanda suka samu rauni a harin wanda aka kai yankin Gari Ya Waye na unguwar Rukuba a birnin na Jos.

    Kwamishinar yaɗa labarai na jihar Filato Joyce Lohya Ramnap ta ce gwamnati ta yi Allah-wadai da "mummunan harin kan mutanen da ba su ji ba, ba su gani ba".

    Sanarwar da kwamishinar ta fitar ta ce dokar ta fara aiki ne daga tsakar dare a ranar Lahadi, kuma za ta ci gaba da aiki har ranar ɗaya ga watan Afrilun 2026.

    Gwamnati ta ce ta ɗauki matakin ne domin daƙile taɓarɓarewar matsalar tsaro, sannan jami'an tsaro za su ci gaba da aiki domin gano waɗanda ke da hannu.

    Gwamnati ba ta fitar da alƙaluma game da mutanen da harin ya rutsa da su ba, sai dai rahotanni jaridun cikin gida sun ce an kashe aƙalla mutum 12 yayin da wasu da dama suka tsira da raunukan harbin bindiga, kuma suke samun kulawa a asibiti.