Majalisar dokokin Kamaru na duba yiwuwar wani ƙudurin da zai ƙirƙiri muƙamin mataimakin shugaban ƙasa,
Wannan na daga cikin buƙatun da shugaba Paul Biya ya gabatar a ƙokarinsa na gyara kundin tsarin mulkin ƙasar.
Gwamnatin ƙasar ta ce, matakin na daga cikin alƙawuran da Biya ya ɗauka na ganin ya samar da sauye-sauye da za su inganta harkokin gwamnati.
Wani ƙuduri da BBC ta gani, ya nuna cewa shugaban ƙasa na da hurumin naɗawa ko cire mataimakinsa, kuma shi zai ci gaba da jan ragamar mulki idan shugaban ya mutu, ko ya kasance ba shi da ƙoshin lafiyar gudanar da mulki.
Sai dai kuma, shugaban riƙon ba shi da ikon gyara kundin dokokin ƙasar ko ya yi takarar shugaban ƙasar.
A baya dai, shugaban majalisar dattawa ne ke da ikon ya gaji shugaban ƙasar, amma kuma a wannan sabon ƙudurin an bayyana cewa za a ɗauki matakin ne domin ba majalisar damar maida hankali kan ayyukanta na dokoki.
Sai dai a sabon ƙudurin, za a ci gaba da riƙe ofishin Firaminista, duk da akwai mataimakin shugaban ƙasa.
Bugu da ƙari, za a buƙaci dukkanin masu riƙe da muƙaman siyasa a ƙasar, kama daga shugaban ƙasa da mataimakinsa, da Firaminista, da ministoci da ƴanmajalisa da sauran masu muƙamai a jihohi su bayyana kadarorinsu a farko da kuma ƙarshen wa’adin mulkinsu.
Daga shekarar 1961 zuwa 1972, Kamaru na bin tsarin shugaba mai cikakken iko, domin mutunta dukkanin bangarorin ƙasar da ke amfani da yaren turancin da faransanci
A lokacin, akwai ofishin mataimakin shugaban ƙasa. Amma kuma daga shekarar 1972, aka yi gyaran dokoki, inda aka koma amfani da tsarin Firaminsta.
An daɗe dai ana cece-ku-ce ka wanda zai gaji Biya idan ya bar mulki, kuma har yanzu babu tabbaci game da makomar Kamaru duk da ana kokarin maido da ofishin mataimakin shugaban ƙasa.
Bayan nazari kan ƙudurin ne, ake sa ran ƴanmajalisar ƙasar su kaɗa ƙuri’a kan amincewa da gyaran kundin dokokin ƙasar ko akasin haka.
Jam’iyar Biya ce dai ita ce ke da rinjaye a duka majalisun ƙasar, inda masu sharhi ke ganin akwai alamun za a amince da buƙatar.