Muna sa ran Amruka da Iran za su ci gaba da tattaunawar zaman lafiya - Macron
Shugaban Faransa Emmanuel Macron ya ce yana sa ran Amurka da Iran za su ci gaba da tattaunawar zaman lafiya duk da rikicin da ya sake ɓarke wa tsakanin ƙasashen biyu.
Macron ya bayyana cewa hare-haren da Iran ta kai kan sansanonin sojin Amurka a yankin Tekun Fasha sun saɓa wa yarjejeniyar da aka ƙulla tsakaninsu, yana mai cewa Tehran ta yi kuskure wajen kai irin waɗannan hare-hare.
Sai dai ya jaddada cewa har yanzu akwai damar ci gaba da tarurruka da tattaunawar da aka tsara a ƙarƙashin yarjejeniyar tsagaita wuta ta kwanaki 60 tsakanin Amurka da Iran.
Kalaman Macron sun zo ne bayan da Shugaban Amurka Donald Trump ya ce yarjejeniyar da ke tsakanin kasashen biyu ta rushe sakamakon sabbin hare-haren da suka kai wa junansu.
Shugaban na Faransa ya ce ci gaba da tattaunawa na da muhimmanci wajen hana rikicin ƙara taɓarɓarewa.