An ta haramta haƙar ma'adanai a inda zaftarewar ƙasa ta kashe mutum 107
Gwamnatin Jamhuriyar Tsakiyar Afirka ta dakatar da duk wasu ayyukan haƙar ma'adanai a yankin Zamboi, inda zaftarewar ƙasa ta kashe aƙalla mutum 107.
Ministan haƙar ma'adanai da nazarin ƙasa da duwatsu na ƙasar Rufin Benam ne ya sanar da haka bayan ya ziyarci wurin da lamarin ya faru a ranar Laraba.
Hukumomi ba su bayyana a hukumance adadin mutanen da suka salwanta ba sanadiyyar lamarin.
Wani jami'i a garin Garou-Boulai na kan iyaka ya shaida wa BBC cewa an zaƙulo aƙalla gawarwaki 107 daga cikin ƙasa.
A ɓangare ɗaya ƙasar Kamaru mai maƙwaftaka ta ce lamarin ya rutsa da ƴan ƙasarta, inda gwamnan yankin gabashin ƙasar ya ce ƴan Kamaru aƙalla uku ne suka rasa rayukansu.