Kana amfani da shafin BBC mai bayyana rubutu kawai (babu hoto) domin rage cin data. Idan ana so a ga hotuna da bidiyo sai a koma babban shafinmu.

Koma shafi mai hoto

Samu ƙarin bayani kan shafin tattalin data

KAI TSAYE, Abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya 20/8/2026

Wannan shafi ne da ke kawo muku muhimman abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya na ranar Alhamis 20 ga watan Agustan 2026.

Rahoto kai-tsaye

Abdullahi Bello, Haruna Kakangi

  1. An ta haramta haƙar ma'adanai a inda zaftarewar ƙasa ta kashe mutum 107

    Gwamnatin Jamhuriyar Tsakiyar Afirka ta dakatar da duk wasu ayyukan haƙar ma'adanai a yankin Zamboi, inda zaftarewar ƙasa ta kashe aƙalla mutum 107.

    Ministan haƙar ma'adanai da nazarin ƙasa da duwatsu na ƙasar Rufin Benam ne ya sanar da haka bayan ya ziyarci wurin da lamarin ya faru a ranar Laraba.

    Hukumomi ba su bayyana a hukumance adadin mutanen da suka salwanta ba sanadiyyar lamarin.

    Wani jami'i a garin Garou-Boulai na kan iyaka ya shaida wa BBC cewa an zaƙulo aƙalla gawarwaki 107 daga cikin ƙasa.

    A ɓangare ɗaya ƙasar Kamaru mai maƙwaftaka ta ce lamarin ya rutsa da ƴan ƙasarta, inda gwamnan yankin gabashin ƙasar ya ce ƴan Kamaru aƙalla uku ne suka rasa rayukansu.

  2. Ƙarin ƴan Najeriya 83 sun koma gida daga Afirka ta Kudu

    Ma’aikatar harkokin wajen Najeriya ta ce ƴan ƙasar 83 sun isa birnin Legas daga Johannesburg a yammacin jiya Laraba, a ci gaba da kwashe ƴan ƙasashen waje daga Afirka ta Kudu sanadiyyar zanga-zangar ƙyamar baƙi.

    Ma’aikatar harkokin wajen ta ce wasu mutane ne suka ɗauki nauyin kwaso mutanen na wannan karo bayan da gwamnatin ƙasar ta rufe ƙofar kwaso ƴan ƙasar da ke zaune a Afirka ta Kudun a cikin watan Yuni.

    Gwamnati ta ɗauki nauyin mayar da ƴan ƙasar gida sau biyar tun bayan ƙazancewar zanga-zangar ƙyamar baƙi a ƙasar ta Kudancin Afirka, lamarin da ya tursasa wa ƙasashe da dama kwashe mutanensu.

    Wasu ƙungiyoyi ne a ƙasar suka tsananta matsin-lambba kan duk wasu baƙi, wadanda ba su da halastattun takardun zama su fice daga ƙasar kafin 30 ga watan Satumba.

    Wannan lamari ya haifar da tsamin dangantaka tsakanin ƙasar da sauran ƙasashen nahiyar Afirka.

    Sai dai gwamnatin ƙasar ta yi tir da hare-haren da ake kai wa baƙin, inda ta ce tana ƙara ƙaimi wajen tabbatar da aiki da dokokin shige da fice, da kuma magance kwarar baƙin haure.

    Afrka ta Kudu ta ce ya zuwa yanzu an kwashe baƙi marasa takardu sama da 80,000 daga ƙasar.

  3. Harin Rasha ya kashe mutum 13 a babban birnin Ukraine

    Hukumomin Ukraine sun ce harin makami mai linzami da Rasha ta kai Kyiv, babban birnin ƙasar ya kashe aƙalla mutum 13 tare da jikkata sama da 40.

    Rahotanni sun ce makamai masu linzami 20 ne na Rasha ta yi amfani da su wajen kai harin kan gidaje da wuraren ajiye kaya da wani asibitin yara.

    Yayin da hukumomin ke ci gaba da yin ƙoƙarin ganin an mayar da wutar lantarki a wasu sassan birnin inda wasu mutane da dama suka maƙale a wurin da suke fakewa a birnin.

  4. Zan ƙaƙaba takunkumai kan Iran da masu taimaka mata - Trump

    Shugaban Amurka Donald Trump ya ce zai kaddamar da sabbin takunkuman tattalin arziki kan Iran da duk wata ƙasa da ke taimaka mata ko yin kasuwanci da ita.

    A cikin wani saƙo da ya wallafa a shafukan sada zumunta, Trump ya ce zai dauki matakin ne saboda Iran ta kasa cimma yarjejeniya da Amurka.

    Sai dai bai bayar da cikakken bayani kan matakan ko sunan wata ƙasa da abin zai shafa ba.

    A ranar Litinin ne yarjejeiyar tsagaita wuta ta kwana 60 ta kare ba tare da wata alama da ke nuna za a kawo ƙarshen yaƙin da ake fafatwa tsakanin Iran da Amurkar ba.

  5. Bashin da ake bin Amurka ya zarce dala tiriliyan 40

    Bashin da ake bin Amurka ya zarce dala tiriliyan arba'in, adadi mafi girma na bashin da aka taɓa bin ƙasar.

    Bashin ya nunninka a cikin shekara 10 yayin da ya riƙa ƙaruwa da dala tiriliyan ɗaya duk wata biyar tun daga shekarar 2020.

    Ƙaruwar kashe kudaden gwamnati ciki har da yaƙi da kuma rage haraji na daga cikin dalilan da suka haifar da haka.

    Sai dai shugaba Trump ya ɗora alhakin hakan kan karin kudin ruwa. Ya ce idan ƙasarmu na samun nasara da ci gaba ya kamata kudin ruwa suyi ƙasa saboda hakan zai ƙara tabbatar da munada jajirtacciyar ƙasa.

    Sai dai masana sun fara nuna damuwa kan yadda bashin ke ƙaruwa cikin sauri.

  6. Barka da warhaka!

    Jama'a barkanmu da wannan safiya ta Alhamis a wannan shafin namu na BBC Hausa, inda muke kawo muku muhimman labarai kai-tsaye na abubuwan da ke faruwa a Najeriya, maƙwaftanta da kuma sassan duniya.

    Za ku iya leƙawa shafukanmu na sada zumunta na facebook da X da kuma whatsapp domin karanta wasu labaran da kallon bidiyo da ma tafka muhawara.

    Ku kasance tare da mu.