KAI TSAYE, Abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya 20/8/2026

Wannan shafi ne da ke kawo muku muhimman abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya na ranar Alhamis 20 ga watan Agustan 2026.

Rahoto kai-tsaye

Abdullahi Bello, Haruna Kakangi

  1. Harin Rasha ya kashe mutum 13 a babban birnin Ukraine

    Hukumomin Ukraine sun ce harin makami mai linzami da Rasha ta kai Kyiv, babban birnin ƙasar ya kashe aƙalla mutum 13 tare da jikkata sama da 40.

    Rahotanni sun ce makamai masu linzami 20 ne na Rasha ta yi amfani da su wajen kai harin kan gidaje da wuraren ajiye kaya da wani asibitin yara.

    Yayin da hukumomin ke ci gaba da yin ƙoƙarin ganin an mayar da wutar lantarki a wasu sassan birnin inda wasu mutane da dama suka maƙale a wurin da suke fakewa a birnin.

  2. Zan ƙaƙaba takunkumai kan Iran da masu taimaka mata - Trump

    Donald Trump

    Asalin hoton, Getty Images

    Shugaban Amurka Donald Trump ya ce zai kaddamar da sabbin takunkuman tattalin arziki kan Iran da duk wata ƙasa da ke taimaka mata ko yin kasuwanci da ita.

    A cikin wani saƙo da ya wallafa a shafukan sada zumunta, Trump ya ce zai dauki matakin ne saboda Iran ta kasa cimma yarjejeniya da Amurka.

    Sai dai bai bayar da cikakken bayani kan matakan ko sunan wata ƙasa da abin zai shafa ba.

    A ranar Litinin ne yarjejeiyar tsagaita wuta ta kwana 60 ta kare ba tare da wata alama da ke nuna za a kawo ƙarshen yaƙin da ake fafatwa tsakanin Iran da Amurkar ba.

  3. Bashin da ake bin Amurka ya zarce dala tiriliyan 40

    Donald Trump

    Asalin hoton, Getty Images

    Bayanan hoto, Shugaban Amurka Donald Trump

    Bashin da ake bin Amurka ya zarce dala tiriliyan arba'in, adadi mafi girma na bashin da aka taɓa bin ƙasar.

    Bashin ya nunninka a cikin shekara 10 yayin da ya riƙa ƙaruwa da dala tiriliyan ɗaya duk wata biyar tun daga shekarar 2020.

    Ƙaruwar kashe kudaden gwamnati ciki har da yaƙi da kuma rage haraji na daga cikin dalilan da suka haifar da haka.

    Sai dai shugaba Trump ya ɗora alhakin hakan kan karin kudin ruwa. Ya ce idan ƙasarmu na samun nasara da ci gaba ya kamata kudin ruwa suyi ƙasa saboda hakan zai ƙara tabbatar da munada jajirtacciyar ƙasa.

    Sai dai masana sun fara nuna damuwa kan yadda bashin ke ƙaruwa cikin sauri.

  4. Barka da warhaka!

    Jama'a barkanmu da wannan safiya ta Alhamis a wannan shafin namu na BBC Hausa, inda muke kawo muku muhimman labarai kai-tsaye na abubuwan da ke faruwa a Najeriya, maƙwaftanta da kuma sassan duniya.

    Za ku iya leƙawa shafukanmu na sada zumunta na facebook da X da kuma whatsapp domin karanta wasu labaran da kallon bidiyo da ma tafka muhawara.

    Ku kasance tare da mu.