Kana amfani da shafin BBC mai bayyana rubutu kawai (babu hoto) domin rage cin data. Idan ana so a ga hotuna da bidiyo sai a koma babban shafinmu.

Koma shafi mai hoto

Samu ƙarin bayani kan shafin tattalin data

KAI TSAYE, Yaƙin Iran da abubuwan da ke faruwa a sassan duniya

Wannan shafi na kawo muku abubuwan da ke faruwa a yaƙin da Amurka da Isra'ila ke yi da Iran da kuma sauran muhimman labarai a sassan duniya na 16/04/2026.

Rahoto kai-tsaye

Usman MINJIBIR

  1. Ana fargabar ƴan'ta'adda na shirin kai hare-hare a Abuja - AFP

    Jami'an tsaron Najeriya na cikin shirin ko-ta-kwana sakamakon bayanan sirri da ke nuna cewa ƙungiyoyin ƴan'adda na shirin kaihare-hare kan gine-gine gwamnati a Abuja, babban birnin Najeriya da jihar Neja mai maƙwabtaka.

    Wata wasikar sirri ta cikin gida a hukumar hana fasa ƙwauri ta Najeriya da kamfanin dillancin labarai na AFP ya samu, ta nuna cewa ƴan bindigar na shirin kai wa filin jirgin sama na Abuja da gidan yari da cibiyar tsare mutane ta sojoji duka a Abuja.

    Bayanin na sirri ya yi kama da harin da ƴan bindiga suka kai wa sansanin sojin sama a birnin Niamey na jamhuriyar Nijar abin da ya janyo fargabar yiwuwar hare-haren bai ɗaya a yankin.

  2. Hezbollah ta ce ta harba rokoki zuwa garuruwan Isra'ila

    Ƙungiyar Hezbollah ta ce ta harba jerin rokoki ga Isra'ila da safiyar ranar Alhamis.

    A wani saƙo da ƙungiyar ta wallafa a Telegram, ta ce ta kai hare-hare kan Kiryat Shmona da Kfar Giladi da Misgav Am da kuma Margaliot da ke arewacin Isra'el da ke kusa da kan iyakarta da Lebanon.

    "Wannan martanin zai ci gaba har zuwa lokacin da zaluncin Amurka da Isra'ila a kan ƙsarmu da mutanenmu," in ji saƙon na Hezbollah.

    Kawo yanzu dai Isra'ila ba ta uffan ba.

    Hare-haren na zuwa ne a daidai lokacin da ake ta ƙoƙarin zaman tattaunawa tsakanin Isra'ila da Lebanon wanda bayanai ke nuna Donald Trump ke matsa lambar yin hakan.

  3. Shugaban Faransa na shirin haramta wa ƴan ƙsa da 15 amfani da soshiyal midiya

    Shugaban Faransa na shirin gudanar da wani taro ta hanyar bidiyo, da shugabannin tarayyar Turai, domin ci gaba da matsa lamba don haramta wa duk wani da yake ƙasa da shekara 15 amfani da shafukan sada zumunta.

    Wakilin BBC ya ce Emmanuel macron zai shafe ranar a cibiyar harshen Faransanci ta ƙasa da ƙasa da ke arewacin Paris inda zai ƙaddamar da ranar, kashe intanet -ta ƙasar domin ƙarfafa wa yara gwiwa su riƙa karatu

    Yanzu haka wata doka da za ta buƙaci shedar yawan shekarun mutum kafin ya yi amfani da shafukan na majalisar dokokin Faransa inda ake shirin tabbatar da ita.

    Haka kuma taron zai tattauna wasu hanyoyin na tantance yawan shekarun mutum.

    Ba da daɗewa tarayyar Turai ta ƙaddamar da manhajarta ta tantance shekaru, wadda matasa 'yan shekaru goma sha za su iya amfani da ita domin shiga shafukan sada zumunta.

    Haka kuma manhajar za ta iya dakatar da duk wanda yake ƙasa da shekara 18 daga shiga shafukan batsa da na caca.

  4. Trump ya ce Isra'ila da Lebanon za su yi magana da juna

    Shugaban Trump ya nuna cewa shugabannin Isra'ila da Lebanon za su yi magana da juna, a ranar Alhamis- zaman karon farko a sama da shekara 30.

    A wani sako da ya sanya a shafinsa na sada zumunta Trump ya ce yana kokarin ganin ya samar da 'yar sa'ida a tsakanin kasashen biyu.

    Iran dai ta kafe cewa dole ne a shigar da batun rikicin Isra'ila da Hezbollah a duk wata yarjejeniya da za a yi ta kawo karshen babban yakin Gabas ta Tsakiya.

    A ranar Laraba Firaministan Isra'ila Benjamin Netanyahu, ya ce dakarun kasarsa na ci gaba da matsawa da kai hari kan Hezbollah.

  5. Buɗewa

    Masu bibiyarmu barkan ku da warhaka a shirin shafin kai tsaye na BBC Hausa inda muke kawo muku labarai da rahotanni kan muhimman abubuwan da ke faruwa a yaƙin da Amurka da Isra'ila ke yi da ƙasar Iran da abubuwan da ke faruwa a sauran ƙsashen duniya.

    Yau ma kamar kullum mun dawo da shafin namu kuma da fatan za ku ci gaba da kasancewa da mu. Mun gode