Ana fargabar ƴan'ta'adda na shirin kai hare-hare a Abuja - AFP
Jami'an tsaron Najeriya na cikin shirin ko-ta-kwana sakamakon bayanan sirri da ke nuna cewa ƙungiyoyin ƴan'adda na shirin kaihare-hare kan gine-gine gwamnati a Abuja, babban birnin Najeriya da jihar Neja mai maƙwabtaka.
Wata wasikar sirri ta cikin gida a hukumar hana fasa ƙwauri ta Najeriya da kamfanin dillancin labarai na AFP ya samu, ta nuna cewa ƴan bindigar na shirin kai wa filin jirgin sama na Abuja da gidan yari da cibiyar tsare mutane ta sojoji duka a Abuja.
Bayanin na sirri ya yi kama da harin da ƴan bindiga suka kai wa sansanin sojin sama a birnin Niamey na jamhuriyar Nijar abin da ya janyo fargabar yiwuwar hare-haren bai ɗaya a yankin.