Mutum uku ke neman takarar shugaban ƙasa a PRP
Jam’iyyar adawa ta PRP a Najeriya ta tantance mutum uku da suke neman tikitin takarar shugaban ƙasa a ƙarƙashinta.
Wata sanarwa da sakataren yaɗa labarai na ƙasa na jam’iyyar, Kwamared Muhammed Ishaq, ya fitar ta ce akwai sama da ƴan takara 260 da ke neman muƙamai daban-daban a ƙarƙashin jam’iyyar a Najeriya.
’Yan takarar da PRP ta tantance da ke neman tikitin takarar shugaban ƙasar sun haɗa da Dr. Nnaoke Ufere daga jihar Abia, da Engr. (Dr.) Yakubu Mohammed Kingsley daga jihar Edo, da Donald Duke, tsohon gwamnan jihar Cross River.
Jam'iyar ta ce za ta gudanar da dukkanin zaɓukan fitar da gwanin jam'iyyar a ranar Litinin, 25 ga Mayu, 2026 a sassa daban-daban na ƙasar.