Abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya 30/01/2026

Wannan shafi ne da ke kawo muku abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya na ranar Juma'a 30 ga watan Janairun 2026.

Taƙaitattu

Rahoto kai-tsaye

Haruna Kakangi, Isiyaku Muhammed, Aisha Babangida da Ahmad Bawage

  1. Sojoji sun ce sun kashe ƴan ta'adda 12 a arewa maso gabas

    Sojoji

    Asalin hoton, NDHQ

    Rundunar sojin Najeriya ta ce dakarunta na Operation Haɗin-Kai sun hallaka wasu ƴan ta'adda 12 a jihar Borno da ke arewa maso gabashin Najeriya.

    Hakan na kunshe ne cikin wata sanarwa da kakakin rundunar haɗin gwiwa ta Joint Task Force, Laftanar- Kanar Sani Uba ya fitar, inda ya ce sun kuma samu nasarar ƙwato makamai da dama a samamen da suka kai Buba Dalo.

    Makaman da aka ƙwato sun haɗa da bindigar AK-47 guda huɗu, bindigogin harba jirage masu saukar ungulu da kuma gurneti.

    Kanal Buba ya ce wani samame na daban da sojoji suka kai sansanin ƴan Boko Haram a Gamo, ya ƙara hallaka ƴan ta da ƙayar-bayar shida, tare da lalata kayakinsu.

    Sojojin sun kuma samu nasarar daƙile wani hari da mayaƙan ISWAP suka yi niyyar kai wa garin Sabon Gari a karamar hukumar Damboa a ranar Alhamis.

    Sai dai, wasu sojoji da kuma ƴan sa-kai na Civilian JTF sun rasa rayukansu yayin daƙile harin.

  2. An ɗaure ɗan majalisar dokokin Mali kan laifin zagin shugaban Ivory Coast

    ...

    Asalin hoton, AFP

    An ɗaure wani ɗan majalisar dokokin Mali shekaru uku a gidan yari a makwabciyar ƙasar Ivory Coast bisa laifin zagin shugaban ƙasar Alassane Ouattara, wanda a kwanakin baya ya sake lashe zaɓe karo na huɗu.

    Mamadou Hawa Gassama, wanda ke aiki a majalisar dokoki ta riƙon ƙwarya da gwamnatin mulkin sojan Mali ta kafa, an kama shi ne a watan Yulin da ya gabata yayin da ya tafi ƙasar Ivory Coast.

    Masu gabatar da ƙara sun ce ya bayyana shugaba Alassane Ouattara a matsayin "azzalumi", "makiyin Mali" kuma ya yi kakkausar suka kan shugabancinsa a cikin hirarraki da kafofin sada zumunta na intanet.

    Tun bayan da sojojin Mali suka karɓi mulki a shekarar 2020, dangantaka da Ivory Coast ta yi tsami.

    Ouattara, wanda ke ƙawance da Faransa - wadda kuma ita ce ta yi wa ƙasashen biyu mulkin mallaka - ya yi suka kan ƙwace mulkin da aka yi a Mali da sauran juyin mulkin da aka yi a yammacin Afirka.

    Tun bayan da aka kama ɗan siyasar na Mali a Abidjan a watan Yulin da ya gabata, hukumomi a Bamako ba su ce uffan kan lamarin ba.

  3. IS ta yi iƙirarin kai hari filin jirgin sama a Yamai

    Yamai

    Asalin hoton, AFP via Getty Images

    Wata cibiya mai ayyukan leƙen asiri da ke bibiyar harkokin masu iƙirarin jihadi ta ambato ƙungiyar IS na ɗaukar alhakin kai harin filin jirgin saman Djiori Hamani na Yamai, babban birnin Nijar.

    Gwamnatin mulkin soja a Nijar ta ce an hallaka mahara 20 lokacin farmakin da suka kai, yayin da aka jikkata sojojin ƙasar huɗu.

    Gwamnati ta faɗa ba tare da gabatar da shaida ba cewa Faransa da Benin da Ivory Coast ne suka kitsa harin, sannan ta yaba wa Rasha saboda taimakon da ta bayar wajen wargaza harin.

  4. MDD na fuskantar barazanar durƙushewa saboda rashin kuɗi - Guterres

    ...

    Asalin hoton, Getty Images

    Majalisar Dinkin Duniya na cikin hadarin durƙushewa saboda ƙasashe mambobin ƙungiyar ba su biya kuɗaɗensu ba, in ji shugaban majalisar.

    António Guterres ya ce Majalisar Dinkin Duniya na fuskantar matsalar kuɗi wanda ke “kara zurfafa barazanar rashin iya aiwatar da shirye-shirye”, kuma kuɗin da ke asusunta na iya ƙarewa a watan Yuli mai zuwa.

    A wata wasiƙa da ya aikewa ɗaukacin ƙasashe mambobi 193, Guterres ya ce dole ne su mutunta alƙawarin biyan kuɗaɗen da suka wajaba ko kuma su yi garambawul ga dokokin kudi na majalisar domin gudun durƙushewa.

    Hakan na zuwa ne bayan babbar mai ba da gudummawa ta Majalisar Dinkin Duniya, Amurka, ta ƙi ba da gudummawa a cikin kasafin kudinta na yau da kullun da na wanzar da zaman lafiya, tare da ficewa daga hukumomi da dama da ta kira "barnar dalar masu biyan haraji".

    Ana bin wasu mambobi da dama bashi wasu kuma kawai sun ƙi biyan kuɗaɗen.

  5. Ƴansanda huɗu a Italiya na fuskantar shari'a kan sakaci wajen mutuwar ƴan ci-rani

    Ƴan ci-rani

    Asalin hoton, Getty Images

    Jami'an ƴansanda huɗu da masu gadin bakin teku biyu na fuskantar shari'a a Italiya, kan zargin sakaci wajen nutsewar ƙwale-ƙwalen ƴan ci-rani a shekara ta 2023.

    Aƙalla mutum 94 ne suka mutu lokacin da ƙwake-ƙwalen mai cike da mutane ya daki dutse sannan ya rabe gida biyu a cikin tekun Italiya.

    Yara 35 cikin waɗanda suka rasa ransu.

    Masu gabatar da ƙara sun zargi ƴansanda da jami'an kula da bakin teku da ƙasa ceto ƙwale-ƙwalen da fasinjojinsa, duk da cewa an ayyyana musu lokacin da lamarin ke faruwa sa'o'i bakwai kafin jirgin ruwan ya nutse.

  6. CAN ta soki lamirin masu son a sauke shugaban INEC

    John Hayab

    Asalin hoton, Getty Images

    Ƙungiyar Kiristoci ta Najeriya (CAN) reshen arewacin ƙasar, ta yi watsi da kiran da Majalisar Koli kan harkokin shariar Musulunci ta yi na neman a cire shugaban hukumar zaɓe mai zaman kanta, Farfesa Joash Amupitan.

    Majalisar Shari'ar na zarginsa da ɓangaranci a wani bayani da yayi a baya kafin a naɗa shi shugaban hukumar ta INEC.

    Sai dai, CAN ta ce akwai siyasa a cikin kiran na Majalisar koli ta sharia.

    Shugaban ƙungiyar a shiyyar arewacin Najeriya, rabaren Joseph John Hayab ya shaida wa BBC cewa kundin tsarin mulki ya bai wa kowane ɗan ƙasa ƴancin zaɓar addini, faɗin ra'ayi da shiga kowace irin ƙungiya.

    "Mun lura kamar wasu ƴansiyasa ne ke da matsala da shugaban na INEC shi ya sa suka fake da majalisar shari'a. Wannan sun shiga abin da bai shafe su ba ne ko kuma ana amfani da su don aikata ba daidai ba," in ji rabaren Hayab.

    Ya ƙara da cewa: "kalaman da shugaban INEC ya yi, kalamai ne da ya shafi kare addininsa sai a zo a fake da addini don a cire shi.... idan muka fara haka to akwai matsala a ƙasar nan.

    Ya ce majalisar Koli kan harkokin shariar Musulunci na zargi ne kawai kan abin da ba ta sani ba, inda ya ce su kuma CAN suna zargi kan abin da suka gani.

    "Idan ana son cewa kowa yana da laifi, to babu wanda zai yi aiki a Najeriya.

    "Shugaban INEC ya yi kalaman da ake zarginsa ne shekaru da yawa da suka wuce, ba wai yanzu da ya hau kujerar shugaban hkumar zaɓe ba," in ji rabaren John Hayab.

  7. Kotu ta rusa shugabancin PDP karkashin Tanimu Turaki

    PDP

    Asalin hoton, Getty Images

    Wata babbar kotun tarayya a Ibadan, babban birnin jihar Oyo, ta rusa shuagabancin jam'iyyar PDP karkashin Kabiru Tanimu Turaki.

    Kotun karkashin jagorancin mai shari'a, Uche Agomoh, ta kuma soke babban taron da jam'iyyar za ta gudanar.

    Har ila yau, kotun ta kuma amince da ɓangaren shugabancin riƙon ƙwarya na Mohammed Abdulrahman a matsayin shugaban jam'iyyar, wanda aka ruwaito yana samun goyon bayan ministan babban birnin tarayya, Nyesom Wike - har sai an gudanar da babban taron jam'iyyar.

    Sai dai, a gefe guda ɓangaren Tanimu Turaki ya sha alwashin ɗaukaka ƙara kan hukuncin.

    "Mun tuntuɓi lauyoyin mu don bin hanyoyi da suka kamata wajen ɗaukaka ƙara da kuma kare matsayar mu," in ji Ini Ememobong, kakakin yaɗa labarai na kwamitin zartaswar jam'iyyar.

    Ya ƙara da cewa, duk da hukuncin kotun har yanzu ɓangaren jagorancin Turaki halastacce ne.

  8. An zane ma'aurata a Indonesiya kan laifin aikata zina da shan giya

    ...

    Asalin hoton, Getty Images

    An zane mata da miji sau 140 a Indonesia saboda aikata zina da shan giya abin da ya saba wa dokar Shari’a, wato dokar addinin Musulunci.

    Mata ‘yar shekara 21 ta suma bayan da hukumomi suka faɗi adadin da za a zane ta a bainar jama’a a lardin Aceh.

    ‘Yan sanda mata uku ne suka yi musayar zane macen yayin da take kuka.

    Bayan ta suma, ‘yansandan mata suka ɗauke ta daga dandalin zuwa mota ɗaukar marasa lafiya.

    An zane mutanen ne a ranar Alhamis tare da wasu mutane hudu, ciki har da jami’in rundunar ‘yan sandan addini, waɗanda duk aka same su da laifi na keta dokar Shari’a.

    Zane mutum hanya ce da ake yawan amfani da ita wajen hukunta masu ƙeta dokokin addinin Musulunci a lardin Aceh mai tsananin bin addini, duk da cewa ƙungiyoyin kare haƙƙin bil’adama sun daɗe suna sukar wannan hukunci suna mai cewa rashin jin ƙai ne.

  9. Kotun ƙolin Indiya ta umurci samar da audugar mata kyauta a makarantu

    A wani hukunci na tarihi, kotun ƙolin Indiya ta ce tsaftar lokacin al'ada ga mata, ƴancin ɗan adam ne na dole, inda ta bayar da umurnin dukkanin makarantu su riƙa samar da audugar mata kyauta ga dukkanin ɗalibai mata.

    A wani rubutaccen ƙara da aka shigar kan buƙatar a samar da issasun kayyaykin tsafta a makarantu da wuraren aiki, alƙalan sun bayar da umurnin cewa dukanin gwamnatocin jihohi su samar da audugar mata waɗanda ke ruddidigewa ga ɗaliban.

    Sun ce rashin samar da kayyakin tsafta na lokacin ala'da ga mata na sa yara mata fuskantar wariya da wulaƙanci da kuma zama abin ƙyama.

  10. 'Rasha ba ta kai hari kan makamashin Ukraine ba amma ta ci gaba da farmaki'

    ...

    Asalin hoton, Getty Images

    Shugaban Ukraine, Volodymyr Zelensky ya ce rundunar sojin Rasha ba ta kai hari ba kan cibiyoyin samar da makamashi na ƙasar ba a daren jiya.

    Sai dai ya zargi Moscow da amfani da makamai masu linzami wajen kai hari kan gidajen ajiyan kayayyaki mallakin wani kamfanin Amurka da ke yankin Kharkiv, da kuma ci gaba da kai hare hare kan gidajen alumma.

    Tun da farko Rasha ta ce ta amince ta daina kai hare-hare a Kyiv, babban birnin Ukraine, har zuwa ranar Lahadi, bisa buƙatar shugaba Trump.

    Sai dai mai magana da yawun fadar Kremlin bai fayyace ba ko ana nufin birnin bakiɗaya, ko kuma kawai kan cibiyoyinta na samar da makamashi ba.

    Dmitry Peskov ya ce tabbas Shugaba Trump ya nemi alfarmar shugaba Putin kan a dai na kai hari a Kyiv har nan da 1 ga watan Fabrairu, saboda a samar da yanayi mai kyau na tattaunawa.

  11. Isra'ila ta ce za ta buɗe mashigar Rafah ta Gaza da Masar

    ...

    Asalin hoton, Getty Images

    Isra'ila ta sanar da cewa za ta bude mashigar Rafah ta Gaza da Masar a ranar Lahadi, saboda alummar bangarorin biyu su riƙa shige da fice.

    Ana ganin wannan muhimmin ci gaba ne, a yayin da shirin tsagaita wuta tsakanin Isra'ila da Hamas da Amurka ke jagoranta ya shiga mataki na biyu.

    Sai dai za a taƙaita adadin mutanen da za su riƙa bin mashigar a kullum, amma sake buɗe mashigar zai bai wai dubban Falasɗinawa marasa lafiya da waɗanda aka jikkata damar zuwa ƙasashen waje domin neman kulawar lafiya.

    Isra'ila ta ce za ta tantance duk mazauna Gaza da ke son komawa har sau biyu kafin a basu izinin shiga.

    Falasdinawan da suka fice lokacin yaƙin ne kawai za a bari su sake komawa.

  12. Iran ta ce a shirye take ta tattauna da Amurka amma bisa mutunta juna

    ...

    Asalin hoton, Getty Images

    Ministan harkokin ƙasashen waje na Iran, Abbas Araqchi, ya sake nanata cewa ƙasarsa a shirye take ta tattauna da Amurka, amma kuma bisa mutunta juna.

    Amma ya yi gargaɗin cewa idan Amurka ta kai musu hari, martanin Iran na iya zarta na Amurka da ke barazanar kai wa Iran harin soji idan ta ci gaba da gudanar da shirinta na nukiliya.

    Aragchi ya nanata cewa shirin nukiliyarsu ba dan su cutar da kowa bane.

    Mista Aragchi ya faɗi hakan ne a Turkiyya, wadda ta ke neman shiga tsakani domin daidaita su.

    Ministan harkokin wajen Turkiyya, Hakan Fidan ya ce dawo da tattauna batun nukiliyar na da muhimmanci.

  13. Afrika ta Kudu ta kori jami'in diflomasiyyar Isra'ila

    ....

    Asalin hoton, Getty Images

    Gwamnatin Afirka ta Kudu ta kori babban jami’in diflomasiyyar Isra’ila inda ta ba shi sa'o'i 72 ya bar ƙasar.

    Ma’aikatar hulɗa da ƙasashen waje ta ce wannan mataki ya biyo bayan abin da ta bayyana a matsayin “take haƙƙin dokokin diflomasiyya da ba za a yarda da su ba, wanda ke ƙalubalantar ikon mallakar Afirka ta Kudu kai tsaye.”

    A cikin wata sanarwa, hukumomin Afirka ta Kudu sun zargi gwamnatin Isra’ila da amfani da shafukan sada zumunta wajen harin shugaba Cyril Ramaphosa.

    Sannan sun ce ofishin jakadancin Isra’ila bai sanar da su ba lokacin da manyan jami’an Isra’ila suka ziyarci ƙasar.

    Hukumomin sun ƙara da cewa waɗannan ayyuka suna nuna cin zarafin haƙƙin diflomasiyya kuma suna rage amincewar da ake buƙata tsakanin ƙasashen biyu.

    Sakamakon haka, hukumomin suka ayyana cewa ba sa marhaba da jami'in diflomasiyyar na Isra'ila kuma sun ba shi kwanaki uku ya bar ƙasar.

    Dangantaka tsakanin Afirka ta Kudu da Isra’ila ta tsananta tun bayan da ƙasar ta shigar da ƙara a Kotun hukunta manyan laifuka ta duniya ICJ a shekarar 2023, inda take zargin Isra’ila da aikata kisan kiyashi a Zirin Gaza, abin da Isra’ila ta ƙi amincewa da shi.

    BBC ta tuntubi ofishin jakadancin Isra’ila a Pritoria domin jin ta bakinsa.

  14. Sojojin Najeriya sun ceto wani fasto daga hannun ƴanbindiga a Enugu

    ...

    Asalin hoton, Getty Images

    Rundunar sojin Najeriya ta ce sojojinta tare da haɗin gwiwar ƴan sa kai ta JTF da sauran hukumomin tsaro sun samu nasarar ceto wani fasto da aka sace, Reverend Johnson Anayo Onugwu, a jihar Enugu.

    An sace faston ne daga gidansa dake al’ummar Ezimo, ƙaramar hukumar Udenu, a daren 29 ga Janairu 2026 da misalin karfe 1:00 na dare, yayin da wasu ‘yan bindiga suka mamaye gidansa.

    Sanarwar da rundunar ta fitar ta ce sojojin da ke garin Udenu sun bi sawun masu garkuwa da fasto ɗin ne bisa bayanan sirri da suka samu inda daga bisani suka yi musayar wuta da ƴanbindigar a al’ummar Okpakeke da ke yankin Itabolo.

    Musayar wutar tsakanin sojojin da ƴanbindigar ya yi sanadin mutuwar ɗaya daga ƴanbindigar lamarin da ya bai wa sojoji damar ceto faston cikin nasara.

    Sanarwa ta kuma ce sojojin sun samu nasarar ƙwato bindiga ƙirar AK-47 da mujallu da harsasa.

    Rundunar ta bayyana cewa, za ta ci gaba da jajircewa wajen kare rayuka da dukiyoyin al’umma.

  15. Mece ce makomar mataimakin gwamnan Kano?

    ...

    Asalin hoton, Aminu Abdussalam Gwarzo

    A daidai lokacin da aka ci gaba da tattaunawa kan dambarwar siyasar Kano, yanzu haka hankali ya koma kan makomar mataimakin gwamnan jihar, Aminu Abdussalam, wanda har yanzu bai fito ya sanar da komawa jam'iyyar APC ba.

    Tuni dai jam'iyyar NNPP ta yi Allah-wadai da kiran da wasu suke yi ga mataimakin gwamnan ya sauka daga muƙaminsa, inda ta bayyana cewa tikiti ɗaya ne ya kai su kujerar da gwamna.

    Tun farko, an ruwaito kwamishinan yaɗa labarai na jihar Kano, Ibrahim Waiya yana shawartar mataimakin gwamnan jihar, Aminu Abdussalam Gwarzo, da ya yi murabus daga muƙaminsa sakamakon rashin bin gwamna Abba Kabir Yusuf zuwa jam'iyyar APC.

    Ya bayyana haka ne a lokacin da yake zantawa da manema labarai a Kano a ranar Alhamis da ta gabata, inda ya ce tafiyar da mulki na buƙatar cikakken aminci da fahimtar juna tsakanin shugabanni.

  16. Amurka ta ayyana Cuba a matsayin barazana ga tsaronta

    ...

    Asalin hoton, Getty Images

    Shugaban Amurka, Donald Trump ya ayyana Cuba a matsayin barazana ga tsaron ƙasarsa, inda ya sanya hannu kan wata doka ta zartarwa, da ta ba da damar sanya harajin cinikayya ga kowace ƙasa da ke sayarwa ko samar da mai ga ƙasar da ke tsibirin Karebiyan.

    Dokar ta ce cibiyar makamashi mafi girma ta Rasha da ke ƙasashen waje na a kasar ta Cuba, baya ga tallafawa da kuma taimaka wa ƙungiyoyin ta'addanci na ƙasashen waje, kamar Hamas da Hezbollah, da kuma ƙasashen da ke adawa da Amurka, ciki har da Rasha, da China da kuma Iran.

    Gwamnatin Trump na ƙoƙarin toshe duk wasu hanyoyin samar da mai ga Cuba, ciki har da ɗaya daga cikin tsoffin masu samar mata da mai, wato Venezuela

    Wata muhimmiyar ƙasa da itama ke samar da mai ga Cuba ita ce Mexico, wannda ita ma a farkon wannan makon ta ce za ta daina samar da mai ga makwabciyar ta ta.

  17. Chadi da Faransa sun amince da ƙarfafa dangantakar tattalin arziƙisu

    ...

    Asalin hoton, Getty Images

    Ƙasashen Chadi da Faransa sun amince da ƙarfafa dangantakar tattalin arzikinsu ta hanyar farfado da haɗin gwiwa bisa ga “girmamawa da muradin juna.” kamar yadda gidan jaridar Alwihda Info mai zaman kansa ya ruwaito.

    Shugaban ƙasar Chadi, Mahamat Idriss Deby Itno, ya gana da takwaransa na Faransa, Emmanuel Macron, a birnin Paris ranar 28 ga Janairu a wata “ziyara ta abota da aiki.” inda ya tafi ƙasar bisa gayyatar Macron.

    “Cikin wannan tsarin, shugabannin ƙasashen biyu sun amince da jerin shawarwari da za su zama taswirar farfado da haɗin gwiwar Faransa da Chadi a fannoni da suke da muradin juna,”.

    Haka kuma, rahoton ya bayyana cewa sun yi alƙawarin ci gaba da tattaunawa don tabbatar da aiwatar da shirin.

    A watan Nuwambar 2024 ne dai dangantaka tsakanin ƙasashen biyu ta yi tsami lokacin da Chadi ta kawo ƙarshen yarjejeniyar soji da Faransa, wanda ya sa Faransa ta janye sojojinta.

  18. Mayaƙan Iswap sun kashe sojojin Najeriya a harin jirage marasa matuƙa

    Army

    Asalin hoton, HQ Nigerian Army

    Rundunar tsaron Najeriya ta tabbatar da cewa mayaƙan Iswap sun kai hari kan sojojinta a garin Sabon Gari da ke jihar Borno a arewa maso gabashin ƙasar.

    Rundunar ta ce an kai harin ne a ranar Alhamis ɗin da ta gabata, kuma ta ƙara da cewa mayaƙan sun yi amfani ne da jirage marasa matuƙa.

    A sanarwar da rundunar tsaron ƙasar ta fitar, ta ce hare-haren sun yi sanadiyar mutuwar wasu sojoji da ba ta bayyana adadinsu ba.

    Mai magana da yawun rundunar, Sani Uba, ya ce an kai harin ne a wani sansanin soji da ke yankin, amma ya ce, "sojojin sun daƙile harin, sannan komai ya lafa."

    A sanarwar da ya fitar a ranar Alhamis, Mr Uba ya ce kafin harin, sojojin na Najeriya sun kai hare-hare a yankin Bulo Dalo, inda a cewarsa suka kashe mayaƙa 12, sannan suka kai wani harin a garin Garno shi ma na jihar ta Borno duka a ranar Laraba, inda a cewarsa a can ma suka kashe mayaƙan guda shida.

    Ya ƙara da cewa sojojin sun ƙwace makamai da alburusai.

  19. Venezuela ta amince da dokar amincewa da masu zuba hannun jari a ɓangaren fetur

    Venezuela

    Asalin hoton, AFP via Getty Images

    Shugabar rikon Ƙwarya ta Venezuela, Delcy Rodriguez, ta sanya hannu kan wata doka da ta ba wa masu sha'awar zuba jari na kasashen waje damar shiga a dama da su, wani abu da canza tsarin gwamnati na shekaru da dama.

    Ana zargin dai Amurka ce ta tilasta yin hakan, bayan ta kama Shugaba Nicolas Maduro a farkon wannan watan, inda yanzu haka yake fuskantar shari'a a ƙasar.

    Shugaba Rodríguez ta bayyana wannan sauyi a matsayin mai cike da tarihi. Yayin da take sanar da matakin ga ƴan ƙasar a wani jawabi da ta gabatar ta talabijin, ta nuna dama can wanda ta gada Nicolas Moduro ya tsara yin hakan kafin a kama shi.

    Tun da farko, Mista Trump ya ba da umarnin bude sararin samaniyar kasar ga jiragen saman yan kasuwa.

  20. Gwamnatin Burkina Faso ta rushe jam'iyyun siyasa a ƙasar

    Traore

    Asalin hoton, Getty Images

    Gwamnatin sojin Burkina Faso ta rushe jam'iyyun siyasa da ƙungiyoyi a ƙasar. Dama can tun a shekarar 2022 ne aka dakatar su, sannan kuma za a miƙa duka ƙadarorinsu zuwa ga gwamnatin ƙasar, kamar yadda kafar gwamnatin ƙasar RTB TV ta ruwaito.

    An amince da dokar rushe jam'iyyun ne a zaman majalisar zartarwar ƙasar, wanda shugaban sojin ƙasar, Ibrahim Traore ya jagoranta.

    Mai magana da yawun gwamnatin ƙasar, Pingdwende Gilbert Ouedraogo ya ce an ɗauki matakin ne bayan nazarin da aka yi kan rahoton binciken da aka gudanar domin inganta harkokin gwamnatin ƙasar, kamar yadda kafar Lefaso.net mai zaman kanta ta ruwaito.

    Kafin juyin mulkin watan Satumban 2022 a ƙasar, akwai jam'iyyun siyasa kusan 100 a ƙasar, inda guda 15 a ciki suke da wakilai a majalisar.