'Iran ta karɓi sabon daftarin yarjejeniyar kawo ƙarshen yaƙi'
Kafar talabijin ta ƙasar Iran ta ce gwamnatin ƙasar ta karɓi daftarin farko-farko na yarjejeniyar fahimtar juna da Amurka kan yadda za a kawo ƙarshen yaƙin da ake yi tsakanin ƙasashen biyu.
Kafar yaɗa labaran ta gwamnati ta ce yarjejeniyar ta ƙunshi cewa Iran za ta buɗe mashigar Hormuz ga jiragen ruwa domin su ci gaba da sufuri kamar yadda yake kafin fara yaƙi, a cikin wata ɗaya.
A ɓangaren Amurka kuma, za ta janye duk wasu dakarunta daga kusa da Iran tare da daina toshewar da ta yi wa tashoshin jiragen ruwa na Iran.
Haka nan yarjejeniyar ta ƙunshi cewa Iran da Oman za su zamo ƙasashen da za su riƙa lura da sufurin jiragen ruwa ta Mashigar Hormuz.
Fadar shugaban Amurka ta bayyana yarjejeniyar da kafar talabijin ɗin ta fitar a matsayin "zallar tatsuniya".
Daftarin ya samo asali ne daga tattaunawar da Pakistan ke yi domin shiga tsakanin ƙasashen biyu.