Kana amfani da shafin BBC mai bayyana rubutu kawai (babu hoto) domin rage cin data. Idan ana so a ga hotuna da bidiyo sai a koma babban shafinmu.

Koma shafi mai hoto

Samu ƙarin bayani kan shafin tattalin data

KAI TSAYE, Abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya 01/09/2026

Wannan shafi ne da ke kawo muku abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya na ranar 01 ga watan Satumbar 2026.

Taƙaitattu

Rahoto kai-tsaye

Daga Aisha Babangida da Abdullahi Diginza

  1. Isra'ila ta ce ta kama wani babban jami'in Hamas a Gaza

    Ministan tsaron Isra'ila, Israel Katz, ya sanar da cewa dakarun ƙasarsa sun kama wani babban jami'in ƙungiyar Hamas a Gaza.

    Sanarwar ta zo ne bayan rahotannin da suka bayyana cewa dakarun musamman na Isra'ila tare da wata ƙungiyar Falasɗinawa da Isra'ila ke marawa baya sun gudanar da ayyuka a birnin Gaza.

    A cewar ma'aikatan agaji na yankin, hare-haren sama da Isra'ila ta kai sun kashe yara biyu da wata mata.

    Sai dai rundunar sojin Isra'ila ta ce ta kai hare-hare ne kan wurare da dama domin kawar da barazana, kuma babu wani soja nata da ya jikkata.

    Ministan bai bayyana sunan jami'in Hamas ɗin da aka kama ko yadda aka kama shi ba.

    Ya kuma jaddada cewa ayyukan sojojin Isra'ila a yankin Netiv Hasara da ke kusa da arewacin Gaza na ci gaba ba tare da tsayawa ba.

  2. Farashin man fetur ya ƙara tashi a Najeriya

    An samu ƙarin farashin man fetur a gidajen mai a sassan Najeriya tun daga farkon wannan mako, lamarin da ya sa masu motoci da sauran al'umma ke fuskantar ƙarin kashe kuɗaɗe wajen gudanar da harkokinsu.

    Rahotanni daga gidajen mai daban-daban sun nuna cewa sabon hauhawar farashin ya fara aiki a wasu jihohi tun daga Litinin.

    Masana na cewa tashi da saukar farashin man a kasuwannin duniya na ɗaya daga cikin abun da ya haddasa wannan lamarin.

    Sun ce hauhawar farashin ɗanyen mai na ƙara wa kamfanonin shigo da mai nauyin kudi, abin da ke tilasta musu daidaita farashin da ake sayar da man fetur a cikin gida.

    Tun bayan sanar da sabon farashin, al'umma da dama sun bayyana damuwarsu kan yadda lamarin zai ƙara tsananta matsin rayuwa.

  3. Putin da Pezeshkian sun tattauna dangantakar Iran da Rasha a Kyrgyzstan

    Shugaban Iran Masoud Pezeshkian ya gana da takwaransa na Rasha Vladimir Putin a gefen taron kungiyar Shanghai Cooperation Organization (SCO) da aka gudanar a birnin Bishkek na ƙasar Kyrgyzstan.

    Kamfanin dillancin labaran Iran na IRNA ya ce shugabannin biyu sun duba halin da dangantakar kasashensu ke ciki tare da tattauna hanyoyin ƙara ƙarfafa haɗin gwiwa a fannoni daban-daban.

    Shi ma kamfanin dillancin labaran Rasha TASS ya tabbatar da ganawar, amma bai bayyana cikakkun bayanan tattaunawar ba.

    A wani bangare, kakakin fadar Kremlin Dmitry Peskov ya ce shugaban ƙasar zai samu bayani kan abubuwan da ke faruwa dangane da batun shiga tsakani tsakanin Iran da Amurka.

  4. 'Babu wata ƙungiyar Musulmi da ke shirin kafa hukumar Hisbah a Filato'

    Ƙungiyar Jama’atu Nasril Islam (JNI) a Jihar Filato ta musanta rahotannin da ke cewa akwai wata ƙungiyar Musulmi da ke shirin kafa hukumar Hisbah a ƙaramar hukumar Jos ta Arewa.

    Sakataren ƙungiyar jihar, Dr Salim Musa Umar, ya ce babu wata ƙungiyar Musulmi da ta sanar da irin wannan shiri, yana mai cewa labarin ya samo asali ne daga wasu hotuna da aka ƙirƙira ta amfani da fasahar AI aka yaɗa a kafafen sada zumunta.

    Ya bayyana cewa ba za a iya kafa Hisbah a hukumance ba sai da dokar Majalisar Dokokin Jihar Filato, kuma babu irin wannan doka da gwamnati ta kafa.

    Ƙungiyar ta kuma buƙaci gwamnati da masu amfani da shafukan sada zumunta su riƙa tantance bayanai kafin yaawa domin kauce wa tayar da hankula da kuma kare zaman lafiya a jihar.

  5. An kai hari kan tankokin man Saudiyya biyu a mashigar Hormuz

    Rahotanni sun ce an kai hari kan manyan tankokin dakon mai guda biyu na Saudiyya yayin da suke bi ta mashigar Hormuz a daren Litinin.

    Kamfanonin sa ido kan harkokin jiragen ruwa, Marisax da Kepler, sun bayyana cewa wasu makamai masu linzami da ba a gano waɗanda suka harba su ba ne suka kai wa tankokin hari a tazarar mintuna kaɗan tsakaninsu.

    Bayanan Kepler sun nuna cewa tankokin sun ɗauki ganga miliyan biyu na ɗanyen man Saudiyya daga tashar Juaima da ke gaɓar Tekun Fasha a makon da ya gabata.

    Lamarin ya ƙara tayar da hankula game da tsaro a yankin mashigar Hormuz, wadda ke ɗaya daga cikin muhimman hanyoyin jigilar man fetur a duniya.

  6. Ina aka samo kalmar Takutaha kuma me ya sa ake biki a ranar?

    Wannan maƙala ce da aka rubuta kuma aka wallafa a ranar 12 ga watan Satumban 2025. Yanzu kuma an sake wallafa ta saboda dacewar ranar.

    A wasu biranen ƙasar Hausa, musamman jihar Kano da ke arewa maso yammacin Najeriya, da zarar ranar Maulidin Annabi Muhammad ta zo, ta wuce, hankali yana komawa ne kan bikin Takutaha.

    Ana dai gudanar da bikin Takutaha ne a ranar bakwai daga ranar Maulidi, wato ranar da Hausawa a al'ada suke yin bikin sunan wanda aka haifa.

    A ranar bakwai da haihuwa ne dai aka saba da bikin raɗa suna da yanka da taron bikin na suna idan an samu ƙaruwa.

    Bikin na Takutaha dai yana ɗaukar hankali sosai ne, inda mutane da dama suke bukukuwan shagali da dama, akwai dafe-dafe da yanka, sannan ake hawa domin murnar ranar.

    Sai dai akwai bukukuwan al'ada da dama da ake aiwatarwa a ranar, sannan kuma akwai abubuwa da suke da alaƙa da ibada.

  7. An sami Duane "Keffe D" Davis da laifin kashe Tupac Shakur bayan kusan shekaru 30

    Wata kotu a Las Vegas, jihar Nevada ta Amurka, ta samu tsohon shugaban ƙungiyar 'yan daba Duane "Keffe D" Davis da laifin kashe shahararren mawaƙin rap Tupac Shakur, wanda aka harbe a shekarar 1996.

    Alƙalan kotun sun yanke hukuncin ne bayan shari’ar da ta ɗauki makonni ana sauraron shaidu da hujjoji.

    An same Davis mai shekara 63 da laifin kisan kai na matakin farko tare da amfani da makami.

    Masu gabatar da ƙara sun ce shi ne ya shirya harin da aka kai wa Tupac bayan wata arangama da ta haɗa mawakin da dan uwansa Orlando Anderson a daren da aka kashe shi.

    Tupac Shakur, ɗaya daga cikin fitattun mawaƙan hip-hop a duniya, ya samu raunuka ne yayin harbin da aka yi masa daga cikin wata mota a Las Vegas a ranar 7 ga Satumban 1996.

    Ya rasu kwanaki shida bayan harin yana da shekara 25 kacal, lamarin da ya janyo ce-ce-ku-ce da hasashe tsawon shekaru da dama ba tare da an kama wani ba.

    An sake farfaɗo da binciken kisan ne bayan Davis ya bayyana wasu bayanai a cikin tarihin rayuwarsa da aka wallafa a shekarar 2019.

    Bayan hukuncin kotun, an bayyana cewa zai iya fuskantar ɗaurin rai da rai, yayin da ya ce zai ɗaukaka ƙara kan hukuncin.

  8. EFCC ta kori ma'aikata sama da 40 kan tafka cin hanci

    Hukumar yaƙi da cin hanci da rashawa ta EFCC ta ce ta kori ma'aikatanta sama da 40 cikin shekaru biyu da rabi da suka gabata saboda hannusu a cin hanci da sauran laifukan kuɗi.

    Shugaban EFCC, Ola Olukoyede, ya ce fiye da mutum biyar daga cikin waɗanda aka kora na fuskantar shari'a a kotu, yayin da ake shirya gurfanar da wasu.

    Ya kuma bayyana cewa hukumar ta ƙaddamar da sabbin matakan tabbatar da gaskiya da riƙon amana a cikin ma'aikatanta, yana mai cewa EFCC ba za ta iya yaƙar cin hanci yadda ya kamata ba idan nata jami'an suna aikata irin wannan laifi.

    Haka kuma ya ce hukumar ta ƙwace sama da naira tiriliyan 1.23 da wasu manyan kuɗaɗen ƙasashen waje tsakanin Oktoban 2023 da Yunin 2026.

  9. Tinubu ya yaba da ceto 'yan bautar ƙasa da aka sace a Kogi

    Shugaban Najeriya, Bola Tinubu ya jinjinawa jami'an tsaro bayan ceto mutum 21 da aka sace a jihar Kogi, ciki har da mambobin bautar ƙasa 15.

    Shugaban ya ce haɗin gwiwar sojoji, 'yansanda, jami'an DSS da kuma masu sa-kai ne suka gudanar da aikin ceton, inda aka kuɓutar da waɗanda aka sacen daga maɓoyar masu garkuwa da mutane a dajin Ofu.

    Tinubu ya ce jami'an tsaro na ci gaba da farautar masu garkuwar, yana mai jaddada cewa duk wanda ke da hannu a lamarin zai fuskanci hukunci bisa doka.

    Ya kuma tabbatar da cewa gwamnatinsa za ta ci gaba da ƙoƙarin tabbatar da tsaron rayuka da dukiyoyin 'yan Najeriya.

  10. Za mu aiwatar da yarjejeniya idan har Amurka ta cika alƙawuranta - Iran

    Shugaban Iran, Masoud Pezeshkian, ya ce ƙasarsa za ta koma aiwatar da yarjejeniyar Islamabad nan take idan Amurka ta koma cika alƙawuran da ta ɗauka a ƙarƙashin yarjejeniyar.

    Yayin da yake jawabi a taron Ƙungiyar Haɗin Kan Shanghai, Pezeshkian ya ce Iran a shirye take ta mayar da martani iri ɗaya idan Washington ta mutunta yarjejeniyar.

    A wani ɓangaren kuma, rundunar sojin Iran ta sake gargaɗin ƙasashen yankin cewa za ta kai farmaki ga duk wata ƙasa da aka yi amfani da yankinta wajen kai mata hari.

    Rahotanni sun kuma ce an kai hari kan wani tankar ɗanyen mai a mashigar Hormuz, yayin da Sakataren Sojin Amurka Daniel Driscoll ya yi murabus bayan samun saɓani da Sakataren Tsaro Pete Hegseth.

  11. NAPTIP ta ceto sama da yara 180 da ake safararsu ta hanyar ƙungiyoyin fara hula na bogi

    Hukumar hana fataucin mutane ta Najeriya (NAPTIP) ta ce ta ceto yara sama da 180 da aka yi safararsu daga jihohin Kaduna, Anambra, Benue, Nasarawa da wasu wurare a ƙasar.

    Hukumar ta bayyana cewa wasu ƙungiyoyin masu fataucin yara na yaudarar iyaye ta hanyar bayyana kansu a matsayin ma'aikatan ƙungiyoyin farar hula masu tallafa wa yara da ilimi, sannan su tafi da yaran da sunan ba su ilimi da tallafi.

    A baya-bayan nan, an ceto wasu yara uku da aka kwaso daga Kajuru a jihar Kaduna a wani gini da ke Onitsha ta jihar Anambra, yayin da aka kuma gano wani yaro a hannun wata ma'aikaciyar lafiya.

    NAPTIP ta ce wasu daga cikin yaran da aka ceto an kai su gidajen marayu inda aka rika sayar da su ga mutane da sunan ɗaukar yara reno.

    Hukumar ta ce tana ci gaba da farautar masu hannu a wannan laifi domin gurfanar da su a gaban kuliya.

  12. Sojojin Yemen sun kai wa Houthi hari tare da lalata jiragen ruwansu marasa matuƙi

    Sojojin Yemen sun ce sun kai hare-haren jiragen sama marasa matuƙa kan sansanonin mayaƙan Houthi a yankuna da dama, tare da kai farmaki kan maɓoyarsu da ke yankin Baqim a arewacin lardin Saada.

    A lokaci guda kuma, rundunar ruwan Yemen ta sanar da cewa ta lalata kwale-kwale huɗu marasa matuƙa na ƴan Houthi kusa da tsibiran Hanish da Dhaqr da ke Tekun Bahar Maliya.

  13. Amurka da waɗanda suka taimaka mata a harin Larak za su ɗanɗana kuɗarsu - Iran

    Iran ta yi gargaɗin cewa duk wata ƙasa ko ɓangaren da ya taimaka wajen kitsa ko ya goyi baya ko ya shiga cikin shirin harin da Amurka ta kai tsibirin Larak zai ɗanɗana kuɗarsa kuma za su ɗauki alhakin sakamakon da zai biyo baya.

    Iran ta ƙara da cewa za su kuma fuskanci martani mai tsanani kan abin da suka aikata.

    A wata wasiƙa da jakadan Iran a Majalisar Ɗinkin Duniya ya aike wa Sakatare Janar na MDD da Kwamitin Sulhu, ƙasar ta yi Allah wadai da harin tare da kira ga Amurka da ta daina abin da ta kira take haƙƙin ƙundin tsarin MDD da kuma matakan da ke barazana ga zirga-zirgar jiragen ruwa a Tekun Fasha da mashigar Hormuz.

    Haka kuma, rundunar sojin Iran ta yi gargaɗin cewa za ta mayar da martani kan duk wata ƙasa da aka yi amfani da yankinta wajen kai hare-hare kan Iran.

  14. Assalamu alaikum

    Shafin Kai Tsaye na BBC Hausa na marhaba da ɗumbin masu bibiyar mu a wannan rana ta Talata.

    Kamar kullum wannan shafi zai kawo muku labarai kan abubuwan da ke faruwa a Najeriya sauran sassan duniya.

    Aisha Babangida ce za ta kasance tare da ku a don haka sai ku ci gaba da kasancewa da mu.

    Za ku iya leƙawa shafukanmu na sada zumunta na facebook da X da kuma whatsapp domin karanta wasu labaran da kallon bidiyo da ma tafka muhawara.