KAI TSAYE, Yaƙin Iran da sauran abubuwan da ke faruwa a sassan duniya

Wannan shafi ne da ke kawo muku labaran yaƙin Iran da sauran abubuwan da ke faruwa a sassan duniya, Talata 19/05/2026

  • Sadis Buba
  • Pantami
  • xxx
  • Nafiu Gombe
  • Mace da ƴarta mai lalaurar Autism
  • wata mata
  • BBC reporter

Rahoto kai-tsaye

Nabeela Mukhtar Uba da Usman Minjibir

  1. WHO ta nuna damuwa kan bazuwar cutar Ebola a Congo

    ...

    Asalin hoton, Jospin Mwisha / AFP via Getty Images

    Hukumar lafiya ta duniya, WHO, ta ce a duk lokacin da ta faɗaɗa bincikenta a kan ɓarkewar cutar Ebola a gabashin jamhuriyar Dumukuradiyyar Congo, sai ta gano shedar cewa lalle cutar ta bazu.

    Wakilin BBC ya ce, wani kuma abin damuwa shi ne, a yanzu ta bazu zuwa yankin da ke da yawan jama'a sosai.

    Hukumomin ƙasar ta Kongo sun ce a yanzu mutanen da cutar ta hallaka sun kai sama da 130 - kuma ana samun ƙaruwar mutanen da suka kamu da cutar.

    To amma kuma gwamnatin ƙasar ta ce akwai jami'ai da ke aiki ba dare ba rana domin gano waɗanda ake ganin sun kamu ko sun yi mu'amala da waɗanda suka kamu.

    Hukumar ta lafiya ta buƙaci jama'a da kada su firgita.

    WHO, ɗin ta ce tana ƙoƙarin ganin ta daƙile bazuwar cutar ne ta hanyar taƙaita zirga-zirgar jama'a, da kuma faɗakar da mutane kan janaizar waɗanda suka rasu, ta hanyar da ta dace don gudun yaɗa cutar.

  2. Matasa sun harbe mutum uku a harin masallaci a San Diego

    ..

    Asalin hoton, EPA

    Wasu matasa biyu sun harbe mutum uku maza a wani masallaci da ke San Diego a California ta Amurka a wani hari da ake zargi na nuna ƙiyayya ne, kafin daga bisani su ɗauki rayuwarsu, kamar yadda ƴansanda suka bayyana.

    Lamarin ya faru ne da sanyin safiyar ranar Litinin, sa'oi biyu bayan da mahaifiyar ɗaya daga cikin waɗanda ake zargi ta kira ƴansanda don shaida musu cewa ɗanta ya gudu tare da wani abokinsa kuma da alamu yana tunanin kashe kansa.

    Ƴansanda sun bazama neman matasan biyu lokacin da harin na San Diego ya soma inda suka samu mutum uku da raunuka sanadin harbin bindiga a wajen ginin.

    Jim kaɗan bayan nan sun sake samun wani kiran wayar cewa an ji ƙarar harbin bindiga daga wata mota. Ƴansan sun gano waɗanda ake zargi a mace - masu shekara 17 da 18 cikin wata mota nesa da masallacin.

    Daga cikin matasan akwai wani mai samar da tsaro da ke aiki a masallacin kuma ya taka muhimmiyar rawa wajen kare harin daga munanana, kamar yadda jami'ai suka ce.

    Hukumomi zuwa yanzu ba su tabbatar da sunayen mutanen ba sai dai mai samar da tsaro a masallacin mahaifi ne ga yara takwas, in ji wani da ya san shi wanda ya faɗa wa CBS.

  3. Maraba

    Masu bibiyar wannan shafi na Kai Tsaye, barka da warhaka. Da fatan mun wayi gari cikin ƙoshin lafiya.

    Kamar kullum, za mu ci gaba da kawo maku labarai kan yaƙin Iran da abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sassan duniya.

    Kuna kuma iya zuwa shafukanmu na sada zumunta domin kallon bidiyo da tafka muhawara kan labaran da muka wallafa.