Ana zargin jagoran ƴan adawar Zambia da cin amanar ƙasa

Asalin hoton, AFP via Getty Images
Ƴansandan Zambia sun gurfanar da magudun jam'iyyar adawa na babban zaben shugaban kasa da aka gudanar a wannan watan, wanda ake takaddama a kansa, bisa zargin cin amanar kasa.
An tuhumi Brian Mundubile tare da abokin takararsa, Makebi Zulu, da wasu mutum goma sha shida.
An kama mutum biyu ne a ranar Alhamis bayan da Shugaba Hakainde Hichilema ya matsa wa Majalisar Dinkin Duniya da ke Lusaka lamba kan ta mika su ga hukumomin kasar.
Sun nemi mafaka ne a ofishin Majalisar Dinkin Duniya bayan da jami'an tsaro suka kashe wani tsohon minista tare da kama wasu 'yan siyasa a wani samame.
Mista Mundubile ya yi watsi da zargin gwamnati cewa jam'iyyarsa na shirin tayar da bore domin kifar da gwamnati.
Laifin cin amanar kasa a Zambia na iya haifar da hukuncin daurin rai da rai.





























