KAI TSAYE, Abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya 30/08/2026

Wannan shafi ne da ke kawo muku abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya na ranar Lahadi 30 ga watan Agustan 2026.

Taƙaitattu

  • Tinubu ya tafi hutun mako uku
  • Amurka da Isra'ila maƙiya Musulunci ne - Mojtaba Khamenei
  • Yawan mutanen da ambaliya ta kashe a Nepal da Tibet ya haura 750, sama da 2,500 sun ɓace
  • Ba za mu mutu ba idan ba mu ci gaba da sarrafa uranium ba - Iran
  • Mun samu matsaya da Oman amma ba za mu buɗe Hormuz ba sai Amurka ta cika alƙawurranta - Iran - Iran
Tsallake Bidiyo ka ci gaba
  • Atiku Abubakar
  • NFF
  • Badriyyah Tijjani Kalarawi
  • Ranar Hausa: BBC
  • Danjuma Goje
  • Zainab
  • BBC
  • ABU
  • xxx
  • xxx
  • Khalifa Dokaji
  • Sheikh Jingir
  • Kano
  • Seriki Abbas
  • xxx

Rahoto kai-tsaye

Daga Aisha Babangida da Isiyaku Muhammed

  1. Ana zargin jagoran ƴan adawar Zambia da cin amanar ƙasa

    Zambia

    Asalin hoton, AFP via Getty Images

    Ƴansandan Zambia sun gurfanar da magudun jam'iyyar adawa na babban zaben shugaban kasa da aka gudanar a wannan watan, wanda ake takaddama a kansa, bisa zargin cin amanar kasa.

    An tuhumi Brian Mundubile tare da abokin takararsa, Makebi Zulu, da wasu mutum goma sha shida.

    An kama mutum biyu ne a ranar Alhamis bayan da Shugaba Hakainde Hichilema ya matsa wa Majalisar Dinkin Duniya da ke Lusaka lamba kan ta mika su ga hukumomin kasar.

    Sun nemi mafaka ne a ofishin Majalisar Dinkin Duniya bayan da jami'an tsaro suka kashe wani tsohon minista tare da kama wasu 'yan siyasa a wani samame.

    Mista Mundubile ya yi watsi da zargin gwamnati cewa jam'iyyarsa na shirin tayar da bore domin kifar da gwamnati.

    Laifin cin amanar kasa a Zambia na iya haifar da hukuncin daurin rai da rai.

  2. Mun sake karɓe iko da sansanin sojin 101 da ke birnin Yamai - Gwamnatin Nijar

    ...

    Asalin hoton, Getty Images

    Gwamnatin Nijar ta ce ta sake karɓe iko da Sansanin Sojin 101 da ke birnin Yamai bayan harin da wasu sojoji suka kai kan sansanin da wasu muhimman wurare a babban birnin ƙasar.

    Hukumomi sun ce dakarun da ke biyayya ga gwamnati sun daƙile yunƙurin tare da dawo da zaman lafiya.

    Ƙungiyar Ƙasashen Sahel (AES) ta bayyana harin a matsayin yunƙurin tayar da zaune tsaye da wasu sojoji suka shirya, tana mai cewa an murƙushe shi saboda ƙwarewa da jajircewar dakarun gwamnati.

    Haka kuma talabijin na gwamnati ya wallafa hotunan kama wasu da ake zargin suna da hannu a boren.

    Rasha ta ce dakarunta na African Corps sun taimaka wa sojojin Nijar wajen dƙkile harin.

    Lamarin na zuwa ne a lokacin da gwamnatin Janar Abdourahamane Tiani ke fuskantar matsin lamba daga hare-haren masu iƙirarin jihadi, tare da nuna alamun rashin jituwa a cikin rundunar sojin ƙasar.

  3. Ana kaɗa ƙuri'ar raba-gardama kan ƙara wa shugaban Guinea-Bissau ƙarfin iko

    Coup

    Asalin hoton, AFP via Getty Images

    Masu kada ƙuri'a a Guinea-Bissau za su kada ƙuri'ar raba gardama a yau akan ko za a amince da wani sabon kundin tsarin mulki da zai ƙara wa shugaban ƙasar iko.

    Ƙuri'ar ta zo ne ƙasa da wata goma bayan sojoji sun ƙwace mulki a ƙasar da ke yammacin Afirka.

    An shirya gudanar da zaɓen gama gari a watan Disamba mai zuwa domin mayar da mulkin farar hula bayan juyin mulkin da aka yi a kasar.

    Sai dai babbar jam'iyyar adawa ta ƙi shiga wannan ƙuri'ar raba gardaman.

  4. Jego

    Asalin hoton, Getty Images

    An fara jin ta-bakin masu taimaka wa alƙali a shari'ar Lindsay Clancy, wata mata a jihar Massachusetts ta Amurka da ake tuhuma da kashe ƙananan ƴaƴanta uku a gidansu da ke wani yanki na wajen birnin Boston.

    A wata shari'a da ta ɗauki hankalin jama'ar Amurka, Clancy ba ta musanta cewa ita ce ta kashe yaran nata ba, amma lauyoyinta na cewa bai kamata a ɗora mata alhaki ba saboda tana fama da matsananciyar lalurar ƙwaƙwalwa.

  5. Za mu amfana da yarjejeniyar ɗanyen mai da muka ƙulla da Amurka - Shugabar Venezuela

    Delcy Rodriguez

    Asalin hoton, Getty Images

    Shugabar riƙon ƙwarya a Venezuela, Delcy Rodriguez, ta ce yarjejeniyar man fetur da ƙasarta ta ƙulla da Amurka, wadda aka sanar a ranar Asabar, za ta tabbatar da ci gaba da ikon Venezuela kan albarkatun ƙasarta.

    Ta ce yarjejeniyar, wadda ta bai wa Amurka iko akan fiye da ganga biliyan 65 na man fetur din Venezuela, har tsawon shekaru 25, kuma za ta bunkasa tattalin arzikin ƙasar.

    Rodriguez ta ƙara da cewa yarjejeniyar za ta mayar da dimbin albarkatun mai da iskar gas na Venezuela wata hanyar samar da kuɗaɗen da za a yi amfani da su wajen tallafa wa shirye-shiryen jin daɗi da walwalar jama'a.

    A nasa ɓangaren, shugaban Amurka Donald Trump ya sha alwashin amfani da arzikin man fetur mai yawa na Venezuela, bayan da Amurka ta kama shugaban ƙasar Nicolas Maduro, a watan Janairun da ya gabata.

  6. Turkiyya ta karɓi baƙuncin taron tsaro na farko tsakaninta da Saudiyya da Pakistan

    ...

    Asalin hoton, Getty Images

    Manyan jami'an Turkiyya, Saudiyya da Pakistan za su gana a Istanbul ranar Litinin domin taron farko na kwamitin haɗin gwiwa da aka kafa ƙarƙashin yarjejeniyar Makka da ƙasashen uku suka sanya wa hannu a watan Agusta.

    Ana sa ran ministocin harkokin wajen ƙasashen, ministocin tsaro da kuma hafsoshin rundunonin sojinsu za su halarci taron, wanda zai mayar da hankali kan aiwatar da yarjejeniyar tsaron haɗin gwiwa tsakanin ƙasashen uku.

    Yarjejeniyar ta tanadi cewa duk wani hari da aka kai wa ɗaya daga cikin ƙasashen zai kasance kamar an kai shi ga sauran ƙasashen biyu, tare da ƙarfafa haɗin gwiwar tsaro, daidaita ayyukan soji da kuma bunƙasa masana'antar tsaro ta hanyar haɗin gwiwa wajen samar da makamai da fasahohin kariya.

  7. CAN ta buƙaci a ƙara tsaro a masallatai da coci-coci bayan sace masu ibada a Neja

    ...

    Asalin hoton, CAN/Facebook

    Ƙungiyar Kiristoci ta Najeriya (CAN) reshen jihar Neja ta yi kira ga hukumomin tsaro da su ƙara ɗaukar matakan kariya a wuraren ibada, musamman lokacin sallar Juma’a da kuma bautar ranar Lahadi, bayan sace wasu masu ibada Musulmai da mazauna yankuna a ƙaramar hukumar Borgu.

    Shugaban CAN a jihar Neja kuma Bishop na Cocin Katolika na Kontagora, Bulus Yohanna, ya ce hare-haren da ake kai wa wuraren ibada barazana ce ga al’umma baki ɗaya, ba tare da la’akari da addinin waɗanda abin ya shafa ba.

    Ya kuma nuna alhini tare da jajanta wa al’ummomin Musulmin da abin ya rutsa da su.

    Kiran na CAN ya biyo bayan harin da ake zargin 'yan ta’adda ne suka kai wasu ƙauyuka a gundumar Dekara da ke Borgu, inda suka yi garkuwa da masu ibada daga masallatai yayin sallar Juma’a.

    Hukumomin tarayya da na jihar Neja sun ce suna aiki tare da jami’an tsaro domin ceto waɗanda aka sace da kuma dawo da zaman lafiya a yankin.

  8. 'Batun takunkuman Amurka kan Iran ne zai mamaye taron G20'

    ...

    Asalin hoton, Getty Images

    Ministocin kuɗi da gwamnonin manyan bankunan ƙasashen G20 za su gana a birnin Asheville da ke jihar North Carolina ta Amurka a ranakun 29 da 30 ga watan Satumba, inda ake sa ran batun takunkuman da Washington ke ƙaƙaba wa Iran zai kasance cikin muhimman batutuwan taron.

    Wani jami'in Ma'aikatar Kuɗi ta Amurka ya ce Washington za ta yi amfani da taron wajen jaddada muhimmancin bin takunkuman da ta sanya wa Iran.

    Haka kuma ana sa ran Sakataren Kuɗi na Amurka, Scott Besant, zai tattauna kai tsaye da takwarorinsa kan yadda ake aiwatar da shirin matsin tattalin arziki kan Tehran, tare da yin gargaɗin cewa kamfanoni da ƙasashen da ke ci gaba da hulɗa da Iran na iya fuskantar hukunci, ciki har da hana su amfani da tsarin dalar Amurka.

    Amurka ta ce tawagogi daga ma’aikatun kuɗi, harkokin wajen ƙasa da tsaro na ci gaba da tattaunawa da gwamnatoci a faɗin duniya domin ƙayyade lokacin kawo ƙarshen ayyukan da ke da alaƙa da Iran.

    G20 dai ya ƙunshi ƙasashe 19 tare da Tarayyar Turai da Tarayyar Afirka, kuma an kafa ƙungiyar ne domin ƙarfafa zaman lafiyar tattalin arziki da harkokin kuɗi a duniya.

  9. Harin Rasha kan ma’ajiyar makamai kusa da Kyiv ya hallaka mutum 37

    ...

    Asalin hoton, Getty Images

    Akalla mutum 37 ne suka mutu yayin da kusan 400 suka tsere daga gidajensu bayan wani harin jirage marasa matuƙa na Rasha ya afkawa wata ma’ajiyar makamai ta sojojin Ukraine a wajen birnin Kyiv.

    Harin, wanda ya faru a daren Juma’a, ya haddasa fashewar harsasai, nakiyoyi da jiragen yaƙi marasa matuƙa da aka adana a wurin.

    Fashewar ta lalata gidaje kusan 130 da ke kusa, ciki har da cibiyar kula da tsofaffi da masu nakasa. Haka kuma mutum 42 sun jikkata, ciki har da yara huɗu.

    Shugaban Ukraine Volodymyr Zelensky ya ce bai kamata a ajiye makamai masu fashewa kusa da gidajen jama’a ba, yana mai bayyana lamarin a matsayin sakaci mai girma.

    Ya kuma sanar da fara bincike kan jami’an da suka amince da adana makaman a yankin da mutane ke zaune, yayin da ayyukan ceto ke ci gaba a yankin Bucha da abin ya shafa.

  10. Tinubu ya tafi hutun mako uku

    ...

    Asalin hoton, Getty Images

    Shugaban Najeriya Bola Ahmed Tinubu zai bar Abuja domin fara hutun mako uku a Turai a matsayin wani ɓangare na hutunsa na shekara-shekara.

    Sanarwar da Fadar Shugaban Ƙasa ta fitar ta ce shugaban zai fara ziyartar birnin London na Birtaniya kafin ya ci gaba da hutun nasa.

    A cewar mai bai wa shugaban shawara na musamman kan yaɗa labarai da dabarun sadarwa, Bayo Onanuga, hutun zai kasance ne a matsayin hutun aiki, inda shugaban zai ci gaba da gudanar da wasu ayyukan gwamnati yayin da yake wajen ƙasar.

    Sanarwar ta ƙara da cewa ana sa ran Shugaba Tinubu zai dawo Najeriya bayan kammala hutun domin shiga zafafan shirye-shiryen yaƙin neman zaɓen shugaban ƙasa na watan Janairun 2027.

  11. Amurka da Isra'ila maƙiya Musulunci ne - Mojtaba Khamenei

    ...

    Asalin hoton, Getty Images

    Jagoran addinin Iran, Mojtaba Khamenei ya ce Amurka da Isra'ila maƙiya ne ga al'ummar Musulmi baki ɗaya ba wai ga Iran da ƙungiyoyin gwagwarmayar Musulunci kaɗai ba,

    A cikin saƙon, Mojtaba Khamenei ya ce shugabannin Amurka da Isra'ila suna adawa da Iran amma ya jaddada cewa adawarsu ta shafi al'ummomin Musulmi na Gabas ta Tsakiya da Arewacin Afirka gaba ɗaya.

    Ya kuma ce hatta wasu shugabannin ƙasashen yankin da ake zargin suna hada kai da waɗannan ƙasashe ba su tsira daga wannan adawar ba.

    Ya kuma yi kira ga Musulmai su rungumi haɗin kai, yana mai cewa duk wanda ya aikata abin da zai haddasa rarrabuwar kawuna ko saɓani tsakanin Musulmai, ko da da gangan ko ba da gangan ba, yana taimakawa wajen cimma manufar maƙiya Musulunci.

    Tun daga shekarar 1981 ne ake gudanar da Makon Haɗin Kan Musulmi tsakanin ranar 12 zuwa 17 ga watan Rabi'ul Awwal, lokacin da ake gudanar da tarurrukan ƙasa da ƙasa kan haɗin kan Musulmi.

    Taron Ƙasa da Ƙasa na 40 kan Haɗin Kan Musulmi ya kammala a yau a Tehran.

  12. Yawan mutanen da ambaliya ta kashe a Nepal da Tibet ya haura 750, sama da 2,500 sun ɓace

    ....

    Asalin hoton, Getty Images

    Yawan mutanen da suka mutu sakamakon mummunar ambaliyar ruwa da ta afku a yankunan Nepal da Tibet ya ƙaru zuwa 752, a cewar hukumar rage haɗurran bala’o’i da gudanar da su ta Nepal (NDRRMA).

    Adadin ya ƙaru daga mutum 734 da aka sanar a baya, yayin da jami’ai ke ci gaba da tattara bayanai daga wuraren da bala’in ya shafa.

    Hukumar ta kuma ce adadin mutanen da suka ɓace ya kai 2,502.

    Ana ci gaba da aikin ceto da neman wadanda suka ɓace, amma jami’ai sun ce rugujewar hanyoyi, zaftarewar kasa da kuma tsananin wahalar isa yankunan da abin ya shafa na kawo cikas ga ayyukan agaji.

    Mahukunta sun bayyana cewa yanayin tsaunukan yankin da lalacewar muhimman hanyoyin sadarwa sun sanya kai kayan agaji da tallafi ga wadanda abin ya shafa ya zama “mai matukar wahala”.

    Hukumomi da ƙungiyoyin agaji na cikin gida da na kasa da kasa na ƙoƙarin kai ɗauki ga dubban mutanen da suka rasa matsugunansu sakamakon wannan mummunar ambaliya.

  13. DSS ta nemi a ɗage shari’ar Sowore zuwa bayan zaɓen shugaban ƙasa na 2027

    ....

    Asalin hoton, Getty Images

    Hukumar Tsaron Farin Kaya ta Najeriya (DSS) ta umarci lauyanta, Akinlolu Kehinde (SAN), da ya nemi a ɗage shari’ar da ake yi wa ɗan takarar shugaban ƙasa na jam’iyyar AAC, Omoyele Sowore, kan zargin aikata laifukan intanet har bayan zaɓen shugaban ƙasa na 2027 kamar yadda Gidan talabijin na Channels ya ruwaito.

    A cewar wata majiya mai masaniya kan lamarin, an ɗauki matakin ne domin bai wa Sowore damar gudanar da yaƙin neman zaɓensa ba tare da shari’ar kotu ta hana shi gudanar da harkokinsa na siyasa ba.

    DSS ta shigar da ƙarar ne bayan wasu saƙonnin da Sowore ya wallafa a shafukansa na X da Facebook a watan Agustan 2025, inda ya kira Shugaba Bola Tinubu da suna “mai laifi”.

    Sai dai Sowore ya musanta zarge-zargen da ake masa, yana mai cewa shari’ar na da alaƙa da siyasa kuma an ƙaddamar da ita ne domin takaita masa ‘yancin faɗar albarkacin baki.

    Rahotanni sun ce shugaban DSS, Tosin Ajayi, ya yi wata ganawa da jami’an sashen shari’a na hukumar inda aka yanke shawarar neman ɗage shari’ar bayan da Hukumar Zaɓe ta Ƙasa (INEC) ta ba da damar fara yakin neman zaɓen 2027.

  14. UAE ta fara binciken rassan Bankin Masar bayan matakin Amurka kan Iran

    Babban bankin Hadaddiyar Daular Larabawa (UAE) ya sanar da fara gudanar da bincike na musamman cikin gaggawa kan rassan Bankin Masar da ke ƙasar, bayan matakin Amurka na katse alaƙar bankin da tsarin kuɗin Amurka domin ƙara matsin lamba kan tattalin arziƙin Iran.

    A cikin wata sanarwa, babban bankin na UAE ya ce binciken zai haɗa da zurfafa nazari kan bayanan da suka shafi lokacin da hukumomin Amurka suka ambata a sanarwarsu.

    Bankin Masar, ɗaya daga cikin manyan bankunan gwamnati a ƙasar Masar, ya ce zai tuntuɓi Ma'aikatar Kuɗi ta Amurka domin neman ƙarin bayani tare da ɗaukar matakan da suka dace.

    Bankin ya kuma tabbatar da cewa rassansa da ke UAE na ci gaba da ba abokan hulɗa hidimomin banki bisa ƙa'idojin da suka dace.

    Matakin da Amurka ta ɗauka na daga cikin ƙoƙarin farko a fili na ware tattalin arziƙin Iran, inda Washington ta ce ta gano hanyoyin da gwamnatin Iran da dakarun juyin juya halin Iran ke amfani da su wajen samun kuɗaɗen shiga, tare da gargaɗin cewa ƙasashen da ke taimaka wa Iran za su iya fuskantar irin waɗannan takunkumai.

  15. Ba za mu mutu ba idan ba mu ci gaba da sarrafa uranium ba - Iran

    ...

    Asalin hoton, Getty Images

    Yousef Pezeshkian, ɗan shugaban ƙasar Iran Masoud Pezeshkian, ya ce rayuwar mutanen Iran ba ta dogara ne kan aikin sarrafa da inganta sinadarin uranium ba, yana mai cewa "idan ba mu yi hakan ba, ba za mu mutu ba."

    A cikin wani saƙo da ya wallafa a shafinsa na Instagram, Yousef ya bayyana cewa ba ya adawa da sarrafa uranium, kuma yana biyayya ga duk wata shawara da Majalisar Tsaron Ƙasa ta Iran da kuma jagorancin ƙasar suka yanke.

    Sai dai ya ce ya kamata a fahimci dukkan fa'ida da illa kafin ɗaukar kowace irin shawara.

    Ya ƙara da cewa makamashin nukiliyar Iran ba ya dogara kacokan da aikin inganta uranium, yana mai nuni da cewa har yanzu man fetur ɗin da tashar samar da wutar lantarki ta Bushehr ke amfani da shi ana shigo da shi ne daga Rasha, ba a cikin gida ake samar da shi ba.

    Yousef Pezeshkian ya kuma ce akwai wasu fasahohi da suka fi muhimmanci ga tsaro da gudanarwar ƙasar, amma ba a ba su kulawar da ta dace ba, yana mai cewa Iran ba ta nuna irin wannan ƙwazo wajen bunƙasa waɗannan fannoni.

  16. Mun samu matsaya da Oman amma ba za mu buɗe Hormuz ba sai Amurka ta cika alƙawurranta - Iran - Iran

    ....

    Asalin hoton, Tasnim news agency

    Mataimakin ministan harkokin wajen Iran, Kazem Gharibabadi, ya ce duk da cewa Tehran da Muscat sun cimma matsaya kan samar da wata hanyar wucin gadi ta zirga-zirgar jiragen ruwa a Mashigar Hormuz, Iran ba za ta buɗe mashigar ba har sai Amurka ta cika alkawurran da ta ɗauka.

    Gharibabadi ya jaddada cewa Mashigar Hormuz har yanzu a rufe take, yana mai cewa idan wani jirgin ruwa ya ratsa ta mashigar, sai da izinin Iran.

    A wani labarin da ke da alaƙa da matsin lambar da ake yi wa Tehran, babban bankin Hadaddiyar Daular Larabawa (UAE) ya sanar da binciken rassan Bankin Masar.

    Matakin ya biyo bayan matakin da Washington ta ɗauka na katse alaƙar bankin da tsarin kuɗi na Amurka, a wani yunkuri na ƙara matsin lamba kan Iran.

  17. Assalamu alaikum!

    Masu bibiyar shafin labaran kai tsaye na BBC Hausa,Barkanmu da wannan safiya ta Lahadi.

    Kamar kodayaushe, za mu kawo maku labarai game da abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya.

    Aisha Babangida ce ke fatan kasancewa da ku a daidai wannan lokacin.

    Za ku iya leƙawa shafukanmu na sada zumunta na facebook da X da kuma whatsapp domin karanta wasu labaran da kallon bidiyo da ma tafka muhawara.

    Ku kasance tare da mu.