Yadda aka kuɓutar da ɗalibai da malamai 44 da aka sace a Oyo - Sojoji

Asalin hoton, Getty Images
Rundunar Sojin Najeriya ta ce an kuɓutar da ɗalibai da malamai 44 da aka sace a ƙaramar hukumar Oriire ta jihar Oyo bayan wani samamen haɗin gwiwa da ya ɗauki fiye da wata guda, wanda aka gudanar tare da haɗin gwiwar hukumomin tsaro da na leƙen asiri daban-daban.
Mai magana da yawun rundunar sojin ƙasa, Danjuma Jonah Danjuma, ya ce aikin ya mayar da hankali kan gano waɗanda suka shirya garkuwar da kuma lalata hanyoyin tallafi da maɓoyarsu da ke cikin dajin Old Oyo National Park.
Ya ƙara da cewa kama wasu da ake zargi ya tarwatsa ƙungiyar, lamarin da ya kai ga sakin waɗanda aka sace ba tare da wani sharadi ba.
Tun da farko, mai bai wa Shugaba Bola Tinubu shawara kan harkokin yaɗa labarai, Bayo Onanuga, ya sanar da sakin ɗaliban da malaman tare da wallafa hotunansu a shafinsa na X.
An sace ɗalibai 39 da malamai bakwai a wani hari da aka kai ranar 15 ga Mayun 2026, kuma rundunar sojin ta ce ana kula da lafiyar waɗanda aka ceto kafin a haɗa su da iyalansu.















