Sojojin Najeriya sun kama wata mota ɗauke da miyagun ƙwayoyi a titin Lagos-Calabar
Rundunar sojin Najeriya ta ce dakarunta sun kama wata mota da ke ɗauke da tarin miyagun ƙwayoyi a kan titin Lagos zuwa Calabar bayan samun sahihan bayanan sirri daga wata majiya.
Aikin da aka gudanar a ranar 9 ga Yulin 2026 ya kai ga cafke direban motar tare da ƙwace kayan da ake zargin miyagun ƙwayoyi ne.
Binciken farko ya nuna cewa ana safarar kayan ne zuwa yankin Berger da ke Jihar Legas, amma wanda aka kama ya kasa bayyana masu kayan ko wanda za a kai wa su.
Bayan kammala matakan farko na bincike, an miƙa wanda ake zargi da kuma miyagun ƙwayoyin ga Hukumar Yaƙi da Sha da Fataucin Miyagun Ƙwayoyi (NDLEA) reshen Jihar Legas domin ci gaba da bincike da gurfanar da shi a gaban doka.
Babban Kwamandan Runduna ta 81, Manjo Janar Adebayo Babalola ya kuma buƙaci sojojin da su ƙara zage damtse wajen yaƙi da masu safarar miyagun ƙwayoyi da sauran masu aikata laifuka a yankin da suke kula da shi.