Iran ta ce ta kakaɓo makami mai linzamin da Amurka da harba mata

Asalin hoton, IRNA
Rundunar juyin juya halin Iran IRGC a lardin Lorestan ta ce ta kakaɓo wani makami mai linzami da sojojin Amurka suka harba mata a bayan garin Khorramabad, babban birnin lardin.
Kamfanin dillancin labaran IRNA ya nakalto sashen hulɗa da jama'a na IRGC yana cewa sabon tsarin kariyar sararin samaniya na rundunar ne ya kakkaɓo makamin da safiyar Lahadi a yankin Dareh da ke wajen birnin Khorramabad.
A wani bangare kuma, jami'an tsaron lardin Lorestan sun bayyana cewa wani ɓangare na makamin da Iran ta harba ya faɗo a wani wurin ajiye motoci da ke unguwar zama a birnin Durood, lamarin da ya jawo lalacewar kadarori kaɗan.
Mataimakin jami'in siyasa da tsaro na gwamnatin lardin, Saeed Pourali, ya ce babu wanda ya rasa ransa ko ya jikkata sakamakon lamarin, yana mai jaddada cewa ba a kai wani harin makami mai linzami kan birnin Durood ba.























