KAI TSAYE, Labaran wasannin BBC Hausa na 10 - 16 Agusta 2026

Wannan shafi ne da ke kawo muku Labaran wasannin BBC Hausa na ranakun 10 - 16 Agusta 2026.

Rahoto kai-tsaye

Muhammad Buhari Fagge

  1. Arsenal ta sake nuna sha'awarta kan Ezri Konsa na Aston Villa

    a

    Asalin hoton, Getty Images

    Arsenal ta sake komawa neman ɗan wasan bayan Aston Villa, Ezri Konsa, yayin da take ƙoƙarin ƙarfafa ɓangaren tsaronta kafin rufe kasuwar saye da sayar da 'yan wasa.

    Konsa mai shekaru 28 na ci gaba da hutunsa bayan kammala gasar Kofin Duniya, kuma ba ya tare da tawagar Aston Villa da za ta kara da Paris St-Germain (PSG) a wasan Super Cup na ranar Laraba.

    Tun farko Arsenal ta yi ƙoƙarin sayen ɗan wasan a wannan bazarar, amma cinikin bai samu nasara ba saboda Gunners ta shirya biyan kusan fam miliyan 30 (£30m) ne kawai, yayin da Aston Villa ke ƙimanta ɗan wasan da kusan £60m.

    A kakar wasan da ta gabata, Konsa ya buga wasanni 48 a dukkan gasa, inda ya taimaka wa Aston Villa wajen lashe gasar Europa League.

    Bayan nasarar ɗauko Bruno Guimaraes daga Newcastle United, zakarun Premier League Arsenal sun mayar da hankali kan ƙarfafa tsaro, kuma sha'awarsu ga Konsa na ƙaruwa cikin sauri.

    Abin da ya sa Arsenal ke son Konsa shi ne yadda yake iya taka leda a wurare daban-daban a bayan gida, abin da ke burge masu yanke shawara a filin Emirates.

    Sai dai Arsenal ta fahimci cewa za ta buƙaci ƙara yawan kuɗin tayinta sosai idan tana son samun nasarar ɗaukar ɗan wasan. Duk da haka, har yanzu ba a san ko Aston Villa za ta amince ta sayar da shi a kan kuɗin da bai kai ƙimarta ba.

    Har ila yau, Arsenal na bibiyar Cristian Romero

    Majiyoyi da dama sun shaida wa BBC Sport cewa Arsenal ta kuma yi tattaunawa ta farko da Tottenham Hotspur kan yiwuwar ɗaukar kyaftin ɗin ƙungiyar, Cristian Romero.

    Sai dai ana ganin Tottenham ba ta da niyyar sayar wa Arsenal ɗan wasan mai shekaru 28, musamman saboda tsananin hamayyar da ke tsakanin ƙungiyoyin biyu na arewacin Landan.

    Duk da haka, hakan bai hana Arsenal yin bincike da tattara bayanai game da yiwuwar cinikin ba, wanda idan ya tabbata zai kasance ɗaya daga cikin mafi ban mamaki a kasuwar musayar 'yan wasa ta bana.

  2. Aston Villa na dab da ɗaukar Matteo Ruggeri daga Atletico Madrid

    a

    Asalin hoton, Getty Images

    Aston Villa na gab da kammala cinikin ɗan wasan baya na Atletico Madrid, Matteo Ruggeri.

    Ana ci gaba da tattaunawa kan yarjejeniyar ɗan wasan mai shekaru 24, kuma ana sa ran zai koma Villa Park bayan ya shafe kakar wasa ɗaya kacal a ƙungiyar Atletico Madrid.

    Ruggeri, wanda ke taka leda a matsayin mai tsaron baya na hagu, zai maye gurbin Lucas Digne, wanda ya koma Paris Saint-Germain (PSG) a ranar Lahadi kan kuɗin da aka ruwaito sun kai fam miliyan 8.5 (£8.5m).

    Digne na iya fuskantar tsohuwar ƙungiyarsa ta Aston Villa a wasan Super Cup da za a buga a birnin Salzburg na Austria a ranar Laraba.

    Kocin Villa, Unai Emery, na neman lashe kofin Super Cup na farko a tarihinsa, bayan ya sha kashi a dukkan wasannin ƙarshe uku da ya buga a wannan gasa.

    A wannan bazarar, Villa ta himmatu wajen sake fasalin zaɓuɓɓukan da take da su a gefen hagu na tsaro, inda take neman ɗan wasan da zai ƙara ƙarfi da kuzari a wannan matsayi.

    Haka kuma, ƙungiyar ta nuna sha'awa ga mai tsaron baya na AC Milan, Pervis Estupiñán, wanda ya taɓa aiki tare da Emery a Villarreal.

    A halin yanzu, Ian Maatsen ne ake sa ran zai fara wasa a gefen hagu na Villa a karawar da za ta haɗa su da PSG a filin wasa na Red Bull Arena da ke Austria.

  3. Depay ya zargi Corinthians da karya alkawari bayan kin sabunta kwantiraginsa

    a

    Asalin hoton, Getty Images

    Memphis Depay ya zargi ƙungiyar Corinthians ta Brazil da nuna "halayen da ba za a amince da su ba" tare da karya yarjejeniyar da aka cimma tsakaninsu bayan kulob ɗin ya yanke shawarar kada ya sabunta kwantiraginsa.

    Tsohon ɗan wasan Manchester United da Barcelona ya koma Corinthians ne a shekarar 2024 kan kwantiragin shekaru biyu. Sai dai yanzu ya zama ɗan wasa mai zaman kansa bayan ya ce kulob ɗin ya janye aniyarsa ta tsawaita kwantiragin da tuni aka amince da ita.

    A wani saƙo da ya wallafa a shafukan sada zumunta, Depay ya ce:

    "An amince da wannan sabuwar yarjejeniya kai tsaye daga shugaban kulob ɗin tare da sashen wasanni, shari'a da kuma kuɗi. Amma wasu mutane sun yanke shawarar karya wannan alkawarin."

    Ya ƙara da cewa:"Ban so wannan yanayin ya faru ba, kuma a tsawon wannan lokaci na girmama kulob ɗin. Amma yanzu an tilasta mini in mayar da martani mai ƙarfi domin kare muraduna."

    "A cikin kwanaki masu zuwa zan yi magana a bainar jama'a, amma ku sani cewa ba zan bar wannan hali da ba za a amince da shi ba ya wuce ba tare da ɗaukar mataki ba."

    Depay ya zura ƙwallaye 20 a wasanni 79 da ya buga wa Corinthians, sannan ya taimaka wa ƙungiyar ta lashe Copa do Brasil a shekarar 2025 da kuma Supercopa do Brasil a wannan shekara.

    Ƙungiyar Corinthians, wadda ke matsayi na bakwai a gasar Serie A ta Brazil, ta bayyana cewa dalilin rashin tsawaita kwantiragin ɗan wasan mai shekaru 32 shi ne matsalolin kuɗi.

  4. Ronaldo ya yi wa Messi ta'aziyyar mahaifinsa

    f

    Asalin hoton, Getty Images

    Cikin wani saƙo mai taɓa zuciya da Messi ya wallafa a shafinsa na Instagram game da rashin mahaifinsa da ya yi da kuma makomarsa a kwallon kafa, Messi har yanzu ya bayyana yana cikin jimamin mahaifinsa.

    Saƙon da Messi ya wallafa hotonsa da na mahaifinsa, ya ce kwallo kawai yake yi amma mahaifinsa ne kwarin gwiwarsa.

    Ronaldo ya wallafa ta'aziyyarsa a ƙarƙashin saƙon dan kwallon da ya ci Ballon d'Or sau takwas a tarihi, inda ya ce, "Runguma zuwa ga kai da kuma duka masoyanka a wannan matsanancin yanayi Leo. fatan ƙarfafa gwiwa".

    Ana kallon kamar wannan ne karon farko da wani cikin 'yan wasan da ake ganin ba sa ga maciji da juna ya fito ƙarara ya yi wa ɗan uwansa sako a kafar sada zumunta.

    Sai dai kuma, halin da Messi ke ciki yana buƙatar a nuna masa tausayawa da goyon baya. Da fari ya yi rashin nasara a wasan ƙarshe na Gasar Kofin Duniya a hannun Spain, ƙasa da wata guda kuma ya rasa mahaifinsa wanda ya yi fama da rashin lafiya mai tsayi.

  5. Torres bai je atisaye ba don kammala komawa PSG

    a

    Asalin hoton, Getty Images

    Zakakurin dan wasan Spain na gasar Kofin Duniya, Ferran Torres, ya samu izini daga Barcelona na rashin zuwa atisayen yau domin ya kammala shirye-shiryen komawarsa Paris St-Germain PSG.

    Torres mai shekaru 26 ya zura ƙwallo daya da ta bai wa Spain nasara a karin lokaci a wasan da Spain ta doke Argentina, lamarin da ya taimaka wa ƙasarsa lashe Kofin Duniya na biyu a tarihinta.

    An tsara cewa zai koma atisaye tare da Barcelona a ranar Laraba, amma an amince masa ka da ya halarta don kammala yarjejeniyarsa da PSG.

    Rahotanni na nuna cewa cinikin zai kai darajar sama da fam miliyan 40.

    Torres na da saura shekara guda kacal a kwantiraginsa da Barcelona, kuma wasu magoya bayan kulob ɗin sun nuna rashin jin daɗinsu kan yadda ɗan wasan ya riƙa bayyana yiwuwar barin ƙungiyar a fili.

    Yayin wata tattaunawa da manema labarai a Amurka bayan nasarar Spain a Kofin Duniya, Torres ya ce: "Ina da kwantiragi da Barcelona, amma a ƙwallon ƙafa ba ka taɓa sanin abin da zai faru a gaba."

    Da aka tambaye shi kai tsaye game da alaƙarsa da PSG, ya ce: "Duk lokacin da irin waɗannan manyan ƙungiyoyi suke sonka abu ne mai kyau. Ba ka taɓa sani ba, domin a ƙwallon ƙafa komai na iya canzawa cikin minti ɗaya. Saboda haka dole ne in kasance a shirye ga komai."

    PSG ta lashe gasar Champions League a shekaru biyu da suka gabata, kuma tsohon kocin Barcelona kuma tsohon ɗan wasanta Luis Enrique ne ke jagorantar ƙungiyar.

    Ƙungiyar ta birnin Paris na iya sakin Bradley Barcola a wannan bazarar, yayin da Liverpool ke zawarcin ɗan wasan na gaba.

    Torres ya kasance a Barcelona tun shekarar 2022 bayan ya shafe shekaru biyu a Manchester City. Ya zura ƙwallaye 25 a wasanni 65 da ya buga wa tawagar ƙasar Spain.

  6. Ba ni da tabbas kan ci gaba da ƙwallon ƙafa - Messi

    g

    Asalin hoton, Getty Images

    Tauraron ƙwallon ƙafa na Argentina, Lionel Messi, ya bayyana cewa bai da tabbaci kan tsawon lokacin da zai iya ci gaba da buga ƙwallo bayan rasuwar mahaifinsa, Jorge Messi.

    Jorge Messi, wanda ya rasu a makon da ya gabata yana da shekaru 68 bayan fama da jinya ta dogon lokaci, shi ne ya kasance wakilin ɗansa tun lokacin da Lionel Messi yake da shekaru 14.

    A wani saƙo mai cike da taɓa zuciya da ya wallafa a shafukan sada zumunta, Messi mai shekaru 39 ya bayyana irin baƙin cikin da yake ciki.

    "Ban san abin da zan yi ba idan babu kai. Ban san yadda zan ci gaba da rayuwa ba."

    Messi ya ƙara da cewa: "Abin da na fi yi kawai shi ne buga ƙwallon ƙafa, amma yanzu ban da tabbacin ko zan ci gaba da yin hakan na dogon lokaci."

    Maganganun na Messi sun ƙara jefa ayar tambaya kan makomar aikinsa na ƙwallon ƙafa, yayin da ake ganin rasuwar mahaifinsa ta yi masa babbar illa.

    Jorge Messi ya taka muhimmiyar rawa a rayuwar ɗansa, ba kawai a matsayin uba ba, har ma a matsayin mai kula da harkokin wasansa tun daga ƙuruciya har zuwa lokacin da ya zama ɗaya daga cikin fitattun 'yan wasan ƙwallon ƙafa a tarihin duniya.

  7. Manchester City ta ɗauko mai tsaron raga Rulli daga Marseille

    Rulli

    Asalin hoton, Getty Images

    Manchester City ta kammala daukar mai tsaron ragar Argentina, Geronimo Rulli, daga Marseille.

    Dan wasan mai shekara 34 yana komawa filin wasa na Etihad - inda ya shafe kakar wasa ta 2016-17 ba tare da ya buga wa babban tawagar wasa ko daya ba - bisa yarjejeniyar shekaru biyu.

    A baya, BBC Sport ta rawaito cewa City ta biya kudi har fam miliyan Daya da dubu dari bakwai.

    Yana zuwa ne domin maye gurbin mai tsaron ragar Ingila, James Trafford, wanda ya bar City ya koma Leeds a yarjejeniyar da ta kai har fam miliyan arba’in da biyar, kuma zai kasance mataimaki ga babban mai tsaron raga Gianluigi Donnarumma.

    Rulli Ya buga wa Argentina wasanni takwas kuma ya kasance cikin tawagar da ta lashe gasar cin kofin duniya ta 2022 da Copa America ta 2024, tare da kaiwa wasan karshe na gasar cin kofin duniya ta wannan shekarar.

    Haka kuma, Rulli ya taba buga wa kungiyoyi daban-daban a Turai wasa, ciki har da Real Sociedad, Montpellier, da kuma Ajax.

  8. Manaco za ta raba gari da Paul Pogba

    a

    Asalin hoton, Getty Images

    Ana sa ran dan wasan tsakiyar Faransa Paul Pogba zai bar Monaco yayin da ake ci gaba da tattaunawa kan yiwuwar kawo ƙarshen kwantiraginsa kafin lokaci.

    Pogba da ya lashe Kofin Duniya a 2018 ya koma ƙungiyar ta Ligue 1 a bazarar da ta gabata bayan an ba shi damar dawowa buga ƙwallon ƙafa, bayan dakatarwar da aka yi masa saboda batun amfani da sinadaran da aka haramta.

    Pogba ya sanya hannu kan kwantiragin shekaru biyu, wanda zai ƙare a ƙarshen kakar wasa mai zuwa.

    Sai dai wata majiya ta shaida wa BBC cewa tattaunawa kan yanke kwantaragin da wuri tana gudana, kuma ana sa ran za a kammala ta nan ba da daɗewa ba.

    BBC Sport ta fahimci cewa Pogba yana jan hankalin wasu ƙungiyoyi a gasar Major League Soccer MLS ta Amurka. A baya an taɓa danganta shi da DC United da kuma Inter Miami.

    Amma Pogba ya samu raunin a cinyarsa a sansanin atisayen kafin kakar wasa da Monaco ta gudanar a Ingila a farkon wannan makon, lamarin da ka iya jinkirta komawarsa MLS.

    Har yanzu Monaco ba ta fitar da wata sanarwa kan lamarin ba.

    Kakar wasan Pogba ta farko a Monaco ta fuskanci cikas sakamakon raunuka, amma akwai fatan cewa a wannan kakar zai riƙa taka leda akai-akai a matsayin ɗan wasan tsakiya na Faransa.

    Sai dai sauyin koci, bayan da Filipe Luis ya maye gurbin Sebastien Pocognoli, na iya sa Monaco ta ɗauki wata sabuwar hanya a fagen wasan tsakiya.

    An dakatar da Pogba na ɗan lokaci daga buga ƙwallo har na tsawon shekaru huɗu bayan sakamakon gwajin da aka yi masa ya nuna amfani da sinadarin dehydroepiandrosterone (DHEA) a watan Fabrairun 2024, bayan wani gwajin da aka yi masa tun watan Agustan 2023.

    Pogba ya dage cewa kuskure ne, yana mai cewa an ba shi wani ƙarin sinadari ba tare da saninsa cewa yana ɗauke da haramtaccen sinadari ba.

  9. Akwai alheri tsakanina da Villa amma Man United na gabanta - Tielemans

    a

    Asalin hoton, Getty Images

    Manchester United ta nuna matuƙar sha’awa kan ɗan wasan tsakiyan Belgium tun a shekarar 2019, bayan Tielemans ya baje kolin hazaka a lokacin da yake zaman aro na farko a Leicester City.

    Haka kuma kulob din ya sake ƙoƙarin sayensa a shekarar 2022, bayan da ya shafe lokaci mai tsawo yana jiran Frenkie de Jong ya yanke shawarar ko zai bar Barcelona.

    Sai dai a wannan watan Yuli ne, lokacin da ɗan wasan mai shekaru 29 ke kan aikinsa na gasar Kofin Duniya, kulob din Old Trafford ya yi nasarar ɗaukarsa, bayan ya biya fam miliyan 35 na sharadin sakin sa daga Aston Villa tare da ba shi kwantiragin shekaru biyar.

    Tielemans ya ce:"Sau biyu na yi tattaunawa da kulob din a baya, amma ba a cimma wata yarjejeniya ba.Na kasance cikin kwanciyar hankali sosai. Gaskiya ban yi tsammanin wani abu mai yawa zai faru a wannan bazarar ba. Na fi mayar da hankali ga ƙwallona, da gasar Kofin Duniya, tare da ƙoƙarin yin iya kokarina domin ƙasata.

    Amma ka san cewa a kowace bazara wani abu na iya faruwa, kuma tabbas na san akwai wannan sharadin sakin aiki. Ina matuƙar godiya ga Aston Villa. Ina bin kulob din bashin alheri mai yawa. Babban kulob ne, mun cimma manyan abubuwa tare, kuma sun taimaka mini na dawo kan mafi kyawun matakina.

    Amma akwai wasu kulob din da suke sama da Villa, kuma Manchester United na ɗaya daga cikinsu. Babbar nasara ce ga kowane ɗan kwallo ya samu damar zuwa nan. Wannan yana nuna cewa ka yi abin kirki a rayuwarka ta ƙwallo. Amma ba a nan ne ƙarshen buri na ba. Ina son in samu nasara."

  10. Omar Artan ya isa Austria domin busa wasan UEFA Super Cup

    A

    Asalin hoton, Getty Images

    Lafarin nan da aka hana bizar shiga Amurka a gasar Kofin Duniya da aka kammala a Amurka da Canada da Mexico.

    Omar Artan dan Somalia ya isa birnin Salzburg na Austria domin busa wasan UEFA Super Cup tsakanin Paris Saint-Germain da ta ci Cahmpions Lig da kuma Aston Villa da ta ci Europa Lig.

    Zai zama dan wata nahiya na farko da zai busa wannan wasa, saboda saka masa da Uefa ta yi na abin da aka yi masa a Kofin Duniya.

    Ga wasu nuhinnan abubuwa da ya kamata ku sani game da wasan:

    Gasar UEFA Super Cup wasa ne na shekara-shekara da ake yi tsakanin gwarzuwar UEFA Champions League da kuma ta UEFA Europa League.

    A bana, za a buga wasan ne tsakanin Paris Saint-Germain, wadda ta lashe Champions League sau biyu a jere kuma ita ce gwarzuwar Ligue 1 ta Faransa, da kuma Aston Villa, wadda ta lashe Europa League karo na farko a tarihinta.

    A ina za a buga wasan?

    x

    Asalin hoton, Getty Images

    Kungiyoyin biyu za su kara ne a filin wasa na Red Bull Arena da ke birnin Salzburg na kasar Austria, inda za a fara wasan da karfe 8:00 na dare agogon BST ranar Laraba, 12 ga Agusta.

    Filin wasan, wanda ke daukar mutane kusan 30,000, shi ne gidan kungiyar RB Salzburg. A yayin gasannin UEFA kuma ana kiransa da Stadion Salzburg.

    Ana sauya sunan ne saboda dokokin UEFA da suka shafi tallace-tallace da sunayen masu daukar nauyin gasar, sannan kuma don bambance shi da RB Arena da ke birnin Leipzig na kasar Jamus, wanda ya karbi bakuncin wasan karshe na Europa Conference League na 2026.

    A baya, filin wasan ya karbi bakuncin wasu wasannin rukuni na gasar Euro 2008, tare da wasannin Europa League da dama.

    Saboda haka, Red Bull Arena na Salzburg na daga cikin fitattun filayen wasa a Turai da suka taba daukar manyan wasannin kasa da kasa da na kungiyoyi.

    Wane ne Alkalin wasan?

    a

    Asalin hoton, Getty Images

    Wasan zai kasance karkashin jagorancin alkalin wasa Omar Artan na kasar Somalia, wanda aka shirya zai yi alkalanci a Gasar Kofin Duniya ta 2026 amma jami’an kula da iyakoki a Miami suka hana shi shiga Amurka.

    Artan yana rike da fasfo na diflomasiyya tare da bizar Amurka mai izinin shiga kasa sau daya kacal, amma duk da haka an hana shi shiga kasar.

    UEFA ta bayyana cewa an dauki matakin nada Artan domin wannan wasa ne bayan tattaunawa da Hukumar Kwallon Kafa ta Afirka CAF.

    Artan ne ya lashe kyautar Alkalin Wasa Mafi Kyau na bangaren maza na CAF a shekarar 2025, kuma an sa ran zai zama dan Somalia na farko da zai yi alkalanci a gasar cin kofin duniya.

    Nadin nasa domin jagorantar wasan UEFA Super Cup ya zama wata babbar alama ta girmamawa ga kokarinsa da kuma ci gaban alkalancin kwallon kafa a Somalia da nahiyar Afirka baki daya.

    Su wane suka taba lashe kyautar a baya?

    a

    Asalin hoton, Getty Images

    Daga cikin wasannin UEFA Super Cup guda 50 da aka buga a baya, sau 30 kungiyar da ta lashe babbar gasar kulob-kulob ta Turai (wadda yanzu ake kira UEFA Champions League) ce ta lashe kofin.

    An fara gudanar da wannan wasa a hukumance tun a shekarar 1973. Daga lokacin har zuwa shekarar 1999, ana hada gwarzuwa gasar Turai (European Cup/Champions League) ne da ta European Cup Winners' Cup.

    Bayan an daina gudanar da gasar European Cup Winners' Cup, sai aka maye gurbinta da ta UEFA Europa League, wanda ya fara fuskantar gwarzuwar Champions League a wasan Super Cup.

    Tarihin nasarori

    • Real Madrid ita ce kungiyar da ta fi kowacce nasara a gasar UEFA Super Cup, inda ta lashe kofin sau shida.
    • Liverpool ce kungiyar Ingila mafi nasara a wannan gasa, bayan ta lashe kofin sau hudu.
    • Aberdeen ita ce kadai kungiyar Scotland da ta taba lashe UEFA Super Cup.

    UEFA Super Cup na ci gaba da kasancewa daya daga cikin muhimman wasannin da ke bude sabuwar kakar wasannin kulob-kulob a Turai, inda yake hada zakarun manyan gasannin nahiyar domin fafatawa kan wani babban kofi na musamman.

  11. Za a yi gagarumin kuskure in aka cire Infantino daga Fifa - Trump

    a

    Asalin hoton, Getty Images

    Shugaban Amurka Donald Trump ya ce zai zama “babban kuskure” idan aka cire shugaban Fifa Gianni Infantino daga mukaminsa, duk da matsin lambar da yake fuskanta.

    Goyon bayan da Trump ya nuna ya biyo bayan wata budaddiyar wasiƙa da ƙungiyar ƙwallon ƙafa ta Turai, da ta Arewacin da Tsakiyar Amurka, da kuma Hukumar Ƙwallon Ƙafa ta Asiya suka fitar, inda suka zargi Infantino da cin amana ta hanyar yaudara dangane da shirin Fifa Forward Enterprise da aka dakatar.

    Shirin FFE ya ƙunshi kafa wani sabon kamfani da zai riƙa kula da haƙƙin kasuwanci da sayar da tikitin dukkan gasannin Fifa, ciki har da Kofin Duniya, inda za a sayar da kashi 21 cikin ɗari na hannun jarin kamfanin ga wani kamfanin masu saka hannun jari masu zaman kansu.

    Kalaman Trump su ne karon farko da ya fito fili yana kare Infantino tun bayan da aka bayyana shirin FFE a ranar 28 ga Yuli.

    A rubutunsa a shafukansa na sada zumunta, Trump ya ce:“Fifa za ta yi babban kuskure idan, saboda kowace irin dalili, ta yi tunanin maye gurbin shugaba Gianni Infantino.”

    Ya ƙara da cewa:“Mutum ne mai ban mamaki, kuma shi ne ya jagoranci gasar Kofin Duniya mafi nasara a tarihi, sau huɗu fiye da kowace da ta gabata. Idan ya tafi, ba za a sake samun irin wannan nasara ko riba ba.”

    An gudanar da Kofin Duniya na 2026 ne tare da haɗin gwiwar Amurka, Canada da Mexico a wannan bazarar, inda Spain ta zama zakara bayan ta doke Argentina a wasan ƙarshe.

    Lokacin da aka tambaye shi game da shirin FFE a karo na farko, ranar 31 ga Yuli, Trump ya ce bai tattauna da Infantino kan batun ba.

  12. Chelsea za ta ba da Mudryk aro

    ,

    Asalin hoton, Getty Images

    Chelsea na nazarin duba yiwuwar ba da Mykhailo Mudryk aro ga wani kulob yayin da yake kokarin dawo da cikakken ƙoshin lafiyarsa bayan shafe watanni 20 ba tare da buga ƙwallo ba.

    Dan wasan kasar Ukraine mai shekaru 25 bai buga wani wasa na gasa ba tun watan Nuwamban 2024.

    An dakatar da shi na tsawon shekaru hudu bayan an samu wani haramtaccen sinadari mai suna meldonium a jikinsa lokacin gwaji.

    Sai dai an cimma yarjejeniya domin warware shari’ar da ta shafi amfani da ƙwayoyin ƙara kuzari, kuma dan wasan gefen ya dawo fili inda ya fito daga benci a wasannin sada zumunta na fuskantar kakar wasa da Juventus, AC Milan da Johor Darul Ta'zim a lokacin rangadin Chelsea a nahiyar Asiya.

    A tarurrukan da aka gudanar a ƙarshen rangadin, Mudryk ya amince ya bar Chelsea a matsayin aro kafin ranar rufe kasuwar musayar 'yan wasa ta 1 ga Satumba.

    An gabatar masa da yiwuwar komawa Strasbourg, kulob ɗin da ke ƙarƙashin mallakar BlueCo wanda suke da mamallaki ɗaya da Chelsea, amma Mudryk ya fi son komawa wani kulob a gasar firimiyar Ingila.

    Wasu kulob-kulob da dama ma sun nuna sha'awar ɗaukarsa, ciki har da wasu manyan kungiyoyi a ƙasar Italiya.

    Mudryk har yanzu yana da kwantiragi da Chelsea har zuwa shekarar 2031, bayan da ya koma kungiyar daga Shakhtar Donetsk a shekarar 2023 kan kuɗin kusan fam miliyan 61.

  13. Van de Ven ya tsawaita kwantaraginsa a Tottenham

    a

    Asalin hoton, Getty Images

    Dan wasan bayan Tottenham, Micky van de Ven, ya ce “a bayyane yake irin alkiblar da kulob din ke son dauka” bayan ya sanya hannu kan sabon kwantiragi na dogon lokaci da Spurs.

    Dan wasan na kasar Netherlands ya koma Tottenham daga Wolfsburg a shekarar 2023, inda ya fara sanya hannu kan yarjejeniyar shekaru shida wadda za ta kare a shekarar 2029.

    BBC Sport ta fahimci cewa Van de Ven ya taba yin tunanin makomarsa a arewacin Landan kafin nadin Roberto De Zerbi a watan Maris, wanda ya taka muhimmiyar rawa wajen yanke shawarar dan wasan mai shekaru 25 ya tsawaita zamansa a kulob din.

    Van de Ven ya taimaka wa Spurs lashe gasar Europa League a shekarar 2025, sannan ya kuma zama kyaftin din kungiyar a wasanni shida na karshe na kakar wasan da ta gabata yayin da suka sha da kyar daga faduwa daga gasar Premier League.

    “Tun daga ranar farko da na zo nan, na kasance ina son Spurs,” in ji Van de Ven.

    “Ina son kulob din, ina son magoya baya, kuma na samu ci gaba sosai a nan. A bayyane yake irin alkiblar da kulob din ke son bi, kuma ina son zama wani bangare na wannan tafiya. Ina matukar farin ciki da abin da ke tafe.”

    Kocin Spurs, Roberto De Zerbi, ya bayyana Van de Ven a matsayin:“Daya daga cikin mafi kyawun masu tsaron baya na tsakiya a Turai kuma muhimmin dan wasa a gare mu.”

    Kocin dan kasar Italiya ya kara da cewa:“Muna gina wata kungiyar mai karfi a nan, kuma 'yan wasa irin su Micky muhimman sassa ne na wannan makoma.”

  14. Na shiryawa gasar Premier ta bana - Wirtz

    ,

    Asalin hoton, Getty Images

    Tauraron ɗan wasan Liverpool Florian Wirtz ya bayyana cewa ya shiryawa gasar Premier League ta bana sama da na baya saboda a yanzu ya saba da yanayin wasan Ingila iddan aka kwatanta wadanda suka gabata.

    Wirtz ya koma Liverpool daga Bayer Leverkusen a bara a yarjejeniyar da ta kai fam miliyan 116, inda ya ci ƙwallaye bakwai tare da bayar da taimakon kwallaye 10 a wata kakar da ba ta yi armashi ba ga Liverpool karkashin tsohon kocinta Arne Slot.

    “Tabbas na koyi abubuwa da dama. Na fahimci yadda ake buga ƙwallo a Premier League, kuma ina ganin na fi shiryawa kakata ta biyu saboda yanzu na san yadda komai yake. Ina matuƙar ɗaukin fara kakar wasa mai zuwa,” in ji Wirtz.

    Dan wasan mai shekaru 23 ya ce bambancin salon wasa tsakanin Jamus da Ingila ya taimaka masa wajen samun sabon fahimta.

  15. Aston Villa na duba yiwuwar daukar Palhinha daga Bayern Munich

    a

    Asalin hoton, Getty Images

    Kungiyar Aston Villa na tattaunawa kan yiwuwar daukar dan wasan tsakiya na Bayern Munich, Joao Palhinha.

    Dan wasan na kasar Portugal mai shekaru 31 ya zama wanda Villa ke son dauka bayan Amadou Onana ya samu mummunan raunin gwiwa a kafarsa ta dama yayin da yake buga wa Belgium wasa a Gasar Kofin Duniya.

    Majiyoyi da ke kusa da Palhinha sun bayyana cewa har yanzu bai yanke hukunci ba, amma yana kofarsa a bude take ta komawa Villa Park, wanda ake kallon yana daga cikin mafi zabuka mafi kyawu da dan wasan ke da su a halin yanzu.

    Bayern Munich a shirye take ta saki dan wasan, shekaru biyu bayan ta saye shi daga Fulham kan kudi kimanin fam miliyan 47.4.

    Palhinha ya shafe kakar wasan da ta gabata a matsayin aro a Tottenham, amma kulob din na Landan ya yanke shawarar kada ya saye shi kai tsaye duk da damar yin hakan kan fam miliyan 26.

    An fahimci cewa koci Roberto de Zerbi yana da sha'awar samun Palhinha saboda rawar da ya taka wajen taimakawa Spurs wajen kauce wa faduwa daga gasar championship, sai dai an kasa cimma yarjejeniya da Bayern Munich.

  16. Shin ko Liverpool ta shirya tunkarar Premier bana?

    a

    Asalin hoton, Getty Images

    A karo na biyu a jere a wasannin sada zumunta, Liverpool karkashin jagorancin sabon kocinta Andoni Iraola ta kasa nasara a wasan da ta ci kwallaye biyu.

    Bayan da Liverpool ta yi rashin nasara da ci 4-2 a hannun Leeds United a Chicago ranar 2 ga Agusta, Iraola ya ce wasan ya taimaka masa wajen fahimtar abubuwa da dama game da ƙungiyarsa.

    Sai dai bayan shan kashi da ci 3-2 a gida wajen Monaco a Anfield ranar Lahadi, kocin ɗan asalin Spain ya fito fili ya bayyana cewa har yanzu ƙungiyar tana da jan aiki mai yawa a gabanta.

    Yayin da ya rage makonni biyu kafin fara gasar Premier League, Iraola ya ce 'yan wasansa ba su iya taka leda da zafin naman da yake buƙata tsawon mintuna 90 ba.

    Ya bayyana cewa Liverpool ta taka rawar gani a mintuna 30 na farkon wasan, amma daga baya matakin ƙarfinsu ya ragu.

    A zahiri, wasan farko da Leeds da kuma mintuna 30 na farkon wasan Monaco su ne mafi kyawun lokutan da Liverpool ta nuna a shirye-shiryen kakar wasa mai zuwa a yanzu. Ƙungiyar ta riƙa buga ƙwallo cikin sauri, tana kai hare-hare kai tsaye, tare da matsa lamba sosai.

    Sabbin taurari Florian Wirtz da Alexander Isak ma sun taka leda da nuna ƙwazo yadda ya kamata.

  17. Alvarez ya koma Atletico Madrid bayan hutu

    a

    Asalin hoton, Getty Images

    Julian Alvarez ya koma Atletico Madrid bayan hutun bayan Gasar Kofin Duniya.

    Dan wasan gaba na Atletico Madrid, Julian Alvarez, ya koma kungiyar a yau bayan kammala hutunsa da ya samu bayan Gasar Kofin Duniya.

    Alvarez, wanda manyan kungiyoyi irin su Barcelona, Paris Saint-Germain da Arsenal ke zawarcinsa, na gudanar da gwaje-gwajen lafiyar jiki da na shirin tunkarar kakar wasa tare da wasu takwarorinsa.

    Shi da Alex Baena, Marcos Llorente da Juan Musso su ne 'yan wasa na karshe da suka koma kungiyar bayan kammala gasar a ranar 19 ga Yuli.

    A halin yanzu suna gudanar da gwaje-gwajen lafiya a Cibiyar Kiwon Lafiyar Wasanni ta Babban Mataki da ke Asibitin Jami'ar Vithas Madrid Arturo Soria.

    Bayan kammala gwaje-gwajen, za su hade da sauran 'yan wasan kungiyar a sansanin atisaye na Atletico da ke Majadahonda.

  18. Ƙungiyar masu zuba jari na ci gaba da tattaunawar sayen hannun jari a Liverpool

    a

    Asalin hoton, Getty Images

    Wasu masu zuba jari da suka haɗa da attajirin nan mamallakin kamfanin Amazon, Jeff Bezos, suna daf da cimma yarjejeniya domin sayen kimanin kaso 30% na hannun jarin Liverpool, kamar yadda BBC Sport ta ruwaito.

    Ƙungiyar masu zuba jarin tana ƙarƙashin jagorancin attajirin ɗan kasuwar nan ɗan Birtaniya dan asalin Indiya, Amit Bhatia, kuma ta haɗa da ɗaya daga cikin waɗanda suka kafa Facebook, Eduardo Saverin.

    Mamallakan Liverpool, Fenway Sports Group, sun tabbatar da cewa ƙungiyar ta nuna sha'awar yin wani muhimmin taron zuba jari na ƙaramin kaso a Ƙungiyar Liverpool.

    Bhatia surukin hamshaƙin attajirin ɗan kasuwar Indiya nan ne Lakshmi Mittal. Ya kuma yi aiki a matsayin darekta kuma mai hannun jari a ƙungiyar Queens Park Rangers na tsawon shekara 18 kafin ya sayar da kasonsa a kulob din a watan da ya gabata.

    Shi kuwa Jeff Bezos, wanda ya kafa katafaren kamfanin kasuwancin intanet na Amazon, shi ne na huɗu a jerin masu arziki a duniya.

    A cewar mujallar Forbes, attajirin mai shekaru 62 yana da dukiyar da aka kiyasta ta kai kusan dala biliyan 256 kimanin fam biliyan 192.

    FSG ta sayi Liverpool a shekarar 2010 kan kuɗin da suka kai fam miliyan 300. Tun daga lokacin, ta taɓa sayar da wani ƙaramin kaso na hannun jarin kulob din ga kamfanin zuba jari na harkokin wasanni na duniya, Dynasty Equity.

    BBC Sport ta tuntubi FSG domin jin karin bayani kan sabbin ci gaban da aka samu a tattaunawar, amma kamfanin ya ce ba shi da wani karin bayani da zai bayar a halin yanzu.

  19. Dan wasan Brazil ya faɗa rami lokacin da yake murnar cin kwallo

    a

    Asalin hoton, Getty Images

    Wani ɗan wasan ƙwallon ƙafa na Brazil ya ce “murna ta ɗauke ni” bayan da ya ji rauni yayin da ya tsallake allunan talla lokacin da yake murnar cin ƙwallo, sai kuma ya faɗa cikin wani rami da ke ɗaya gefen.

    Mai tsaron baya Jacy Maranhao, mai shekaru 29, ya ci wa ƙungiyarsa ta Coritiba ƙwallo daya mai ban haushi a wasan da suka buga da Chapecoense da kuma kungiyarsa da ke buga firimiyar Brazil, yayin da ƙungiyarsa ke gaba da ci 1-0 a minti na 41.

    Bayan cin ƙwallon, ya ruga zuwa wajen magoya baya yana murna, inda ya yi tsalle ya haye allon talla, amma nan take ya ɓace bayan ya faɗa cikin wata hanya mai zurfi da ke kaiwa ɗakin sauya kaya na baƙin wasa.

    Ko da yake ya samu damar fitowa da ƙyar daga cikin ramin, inda ya samu rauni a idon sawunsa.

    Abin takaici kuma, an soke ƙwallon da ya ci bayan duba na'urar VAR, a wasan da Coritiba ta yi nasara da ci 2-1. Daga baya an canje shi jim kaɗan bayan an dawo daga hutun rabin lokaci saboda raunin da ya samu.

    Ba wannan ne karo na farko da irin wannan lamari ya faru a filin wasan Couto Pereira Stadium da ke birnin Curitiba ba.

    A shekarar 2014, ɗan wasan Kamaru Joel ma ya yi tsalle ya haye katangar talla bayan cin ƙwallo, sai ya faɗa cikin irin wannan hanyar a wasan da Coritiba ta doke São Paulo da ci 3-1.

  20. Fulham ta saye Shea Charles daga Southampton kan £30m

    a

    Asalin hoton, Getty Images

    Fulham ta amince da yarjejeniyar sayen Shea Charles kan fam miliyan 30.

    Kungiyar Fulham ta cimma yarjejeniya da za ta kai darajar fam miliyan 30 domin daukar dan wasan tsakiya na Southampton, Shea Charles.

    Idan ya wuce gwajin lafiya, dan wasan mai shekaru 22 zai koma Craven Cottage kan kwantiragin shekara biyar, kuma zai zama dan wasan Arewacin Ireland mafi tsada a tarihi.

    Charles, wanda ya fara kwallonsa a Manchester City, ya kuma ja hankalin Leeds United, amma ya zabi komawa yammacin Landan domin maye gurbin Sasa Lukic, wanda ya koma Ipswich Town a makon da ya gabata.

    Zai zama dan wasa na uku da Fulham ta dauka tun bayan nada sabon koci Alvaro Arbeloa, wanda ya jagoranci Real Madrid na rikon kwarya a ƙarshen kakar wasan da ta gabata.

    Zuƙowar Arbeloa bayan tafiyar Marco Silva zuwa Benfica, ya sa Fulham ta dauki 'yan wasa biyu daga Real Madrid, wato ɗan gaba Gonzalo Garcia da ɗan wasan tsakiya Cesar Palacios, kafin yanzu ta kammala yarjejeniyar Shea Charles.