KAI TSAYE, Abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya 23/8/2026

Wannan shafi ne da ke kawo muku muhimman abubuwan da ke faruwa a Najeriya da maƙwaftan ƙasashe da kuma sauran sassan duniya na ranar Lahadi 23 ga watan Agustan 2026.

Tsallake Bidiyo ka ci gaba
  • BBC
  • ABU
  • xxx
  • xxx
  • Khalifa Dokaji
  • Sheikh Jingir
  • Kano
  • Seriki Abbas
  • xxx
  • xxx
  • Bola Tinubu
  • Senator Gaya
  • xxx
  • xxx
  • Zahra Buhari

Rahoto kai-tsaye

Isiyaku Muhammed

  1. Wata hadakar malamai a Arewacin Najeriya ta amince Tinubu ya zarce

    Malamai

    Asalin hoton, Isah Muhammad Yusuf/FB

    Wata hadakar malaman Musulunci daga jihohi 19 na Arewacin Najeriya ta bayyana goyon bayanta ga Shugaba Bola Ahmed Tinubu, tare da amincewa da ya sake tsayawa takara a zaben 2027.

    Hadakar ta bayyana matsayarta ne yayin taronta na Muslim Intellectuals Forum, wanda aka gudanar a dakin taro na Sir Ahmadu Bello, Sabuwar Sakatariya da ke Dutse, Jihar Jigawa.

    Hadimin Gwamnan Jihar Kano, Abba Kabir Yusuf, Isah Muhammad Yusuf, ne ya bayyana hakan a wani sako da ya wallafa a shafinsa na Facebook.

    A cewarsa, taron ya hada malaman Musulunci da masana daga jihohin Arewacin Najeriya 19, inda suka bayyana amincewarsu da jagorancin Shugaba Tinubu da kokarinsa na magance matsalolin da ke addabar yankin, musamman matsalar rashin tsaro.

    Kungiyar ta kuma kada kuri'ar amincewa da Shugaba Tinubu, tare da kira ga 'yan Najeriya, musamman al'ummar Arewa, da su mara wa shugaban baya da jam'iyyar APC a zaben 2027.

    Goyon bayan na zuwa ne a daidai lokacin da jam'iyyu da kungiyoyin siyasa ke kara shirye-shiryen tunkarar babban zaben 2027.

    A nata bangaren, kungiyar ta ce ta yi imanin cewa jagorancin Tinubu da matakan da gwamnatinsa ke dauka za su taimaka wajen magance kalubalen da Arewacin Najeriya ke fuskanta.

  2. Hukumomin tsaron Iran sun gano “na’urorin Starlink 997”

    Starlink

    Asalin hoton, Getty Images

    Farajah, rundunar tsaron Jamhuriyar Musulunci ta Iran, ta ce a cikin watanni huɗu na farkon wannan shekara, ta gano “na’urorin tauraron dan adam na Starlink 997 da kayan haɗa su.”

    Shugaban sashen tattalin arziki na Farajah ya ce: “Tun bayan yaƙin kwana 12, ’yan sanda sun ƙara mai da hankali wajen ganowa tare da kwace na’urorin tauraron dan adam na Starlink da kayan haɗinsu. Dukkan sassan ’yan sanda, daga iyakokin ƙasar har zuwa cikin birane, sun fara aiki sosai a wannan fanni.”

    Hossein Rahimi ya kuma ce: “Dangane da wannan batu, an kama mutum 163, sannan an kwace motoci 15 da ke ɗauke da kayan aikin Starlink.”

    A cewarsa, mafi yawan waɗannan na’urori sun shigo ƙasar ne ta iyakokin yamma da arewa maso yammacin ƙasar, da kuma daga Azerbaijan da yankin Kurdistan. Haka kuma, wasu sun shigo ta iyakokin ruwa na kudancin ƙasar, ciki har da hanyoyin Qatar, Hadaddiyar Daular Larabawa (UAE), da Oman.

    Wannan fasahar tauraron dan adam da ake amfani da ita wajen haɗa mutane da intanet na duniya haramun ce a Iran. Kafofin yaɗa labaran gwamnatin Iran sun ruwaito lokuta da dama na kama mutane saboda mallakar tashoshin Starlink ko saye da sayar da su.

    Cibiyar sadarwar Starlink wata tarin tauraron dan adam ce da aka ƙera domin samar da intanet mai sauri, mai ƙarancin jinkiri, a duk faɗin duniya.

  3. Ƙasar da ta taimaki Amurka a yaƙin tattalin arziki maƙiyarmu ce - Iran

    IRAN

    Asalin hoton, AFP via Getty Images

    Ƙasashen da suka shiga “yaƙin tattalin arziki” na Amurka ana ɗaukar su a matsayin abokan gaba

    Jami’an Iran sun ce duk wata ƙasa da ta shiga abin da suka kira “yaƙin tattalin arziki na Amurka da Iran” za a ɗauke ta a matsayin abokiyar gaba.

    A baya Iran ta kai hari kan wasu ƙasashe a yankin da ke karɓar sansanonin sojojin Amurka, waɗanda daga cikinsu ne aka kaddamar da hare-haren Amurka da dama.

    A halin yanzu, tattaunawa tsakanin Iran da Amurka ta tsaya cik, amma Shugaban Iran, Masoud Pezeshkian, ya bayyana a ranar Juma’a cewa lokaci ya yi da za a kawo ƙarshen rikicin da ya kwashe watanni shida yana gudana.

  4. Barka da warhaka!

    Jama'a barkanmu da wannan safiya ta Lahadi a wannan shafin namu na BBC Hausa, inda muke kawo muku muhimman labarai kai-tsaye na abubuwan da ke faruwa a Najeriya, maƙwaftanta da kuma sassan duniya.

    Za ku iya leƙawa shafukanmu na sada zumunta na facebook, instagram da X da kuma whatsapp domin karanta wasu labaran da kallon bidiyo da ma tafka muhawara.

    Ku kasance tare da mu.