KAI TSAYE, Abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya 29/06/2026

Wannan shafi ne da ke kawo muku abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya na ranar Litinin 29 ga watan Yunin 2026.

Taƙaitattu

Skip Bidiyo and continue reading
  • xxx
  • Ummulkhairi Aliyu
  • xxx
  • xxx
  • xxx
  • xxx
  • Arsenal
  • xxx
  • xxx
  • xxx
  • xxx
  • Kutama
  • xxx
  • Sadis Buba

Rahoto kai-tsaye

Daga Aisha Babangida da Haruna Kakangi

  1. Har yanzu gwamnati ba ta tuntuɓe mu ba - Iyalan Shugaban Miyetti-Allah

    ....

    Asalin hoton, Amnesty International

    Iyalan shugaban ƙungiyar Miyetti-Allah, Alhaji Ardo Risku da aka kashe a jihar Benue sun koka cewa har yanzu gwamnati ba ta tuntuɓe su ba tun bayan faruwar lamarin, duk da alƙawuran da ake yi na cewa za a ɗauki mataki kamar yadda babban ɗan marigayin, Muhammad Idris ya shaidawa BBC.

    Wannan na zuwa ne bayan da rundunar ’yansandan jihar Benue ta tabbatar da kama mutum 10 da ake zargi da hannu a kisan shugaban da wasu mutum uku, wanda aka harbe su a ranar Juma’a yayin da yake kan hanyarsa ta komawa gida daga wani taro da ya shafi tsaron jihar.

    Gwamnatin jihar Benue ta bayyana cewa ta yi allawadai da kisan tare da ƙaddamar da bincike, amma iyalan marigayin sun ce ba su ji wani sakamako kai tsaye daga gwamnati ba

    Sun bayyana cewa har yanzu suna jiran a tuntu be su domin ganin an yi musu bayani kan matakan da ake dauka.

    Babban ɗan ya ce a ranar da aka kashe shi, ya je ya gaishe shi da safe, inda ya shaida masa cewa DPO na karamar hukumar Ohimini ya kira shi domin wani taro. “Sai ya kira wasu mutum uku su tafi tare, suka hau babur suka nufi inda za a yi taron,” in ji shi.

    Ya ƙara da cewa sun samu labarin kisan ne bayan sallar Juma’a, lokacin da suka ga mutane sun taru ana cewa an ga wasu mutane a bakin hanya an harbe su.

    “Mun kira wayoyinsu ba su shiga ba, daga nan muka tafi wurin muka tarar ’yansanda sun riga mu, muka dauki gawarwakin,” in ji shi, yana mai korafin cewa, “tun daga lokacin DPO bai kira mu ba, gwamnatin ma ba ta tuntuɓe mu ba,” tare da jaddada cewa wanda aka kashe ba Fulani kaɗai ba ne, shugaba ne da ya shafi jama’a baki ɗaya.

  2. Ko sakamakon zaɓen 2023 zai iya zama madubin na 2027?

    ...

    Tun bayan da jam'iyyun siyasa a Najeriya suka kammala zaɓukar fitar da gwanayen da za su tsaya musu takara a zaɓukan 2027, wasu ƴanƙasar suka soma hasashen sakamakon zaɓen da ke tafe ta hanyar kwatanta shi da na 2023 da ya gabata.

    Bisa ga bayanan zaɓukan fitar da gwanayen ƴantakarar da suka fatata a 2023 ne za su sake karawa a zaɓen na 2027.

    Hakan ne ma ya sa wasu ƴanƙasar ke amfani da lissafin sakamakon 2023 domin hasashen sakamakon 2027.

    To sai dai masana da masu sharhin siyasar ƙasar na cewa sakamakon 2023 ba zai zama madubin na 2027 ba.

    A watan Janairun 2027 ne dai za a yi zaɓen shugaban ƙasa a Najeriyar, ƙasar da ta fi kowa yawan al'umma a nahiyar Afirka.

  3. Mutum biyar sun mutu, takwas sun jikkata a hatsarin mota a Neja

    An tabbatar da mutuwar mutum biyar, yayin da wasu takwas suka jikkata sakamakon hatsarin mota da ya faru a ranar Lahadi a yankin Agaie da ke ƙaramar hukumar Agaie a jihar Neja.

    Jami’in hukumar ba da agajin gaggawa ta ƙasa (NEMA) a yankin, Hussaini Guregi, ne ya tabbatar da faruwar lamarin ga manema labarai.

    Ya ce hatsarin ya shafi wata babbar mota ɗauke da kimanin fasinjoji 40 da kuma wata tankar mai.

    Motar na kan hanyarta ne daga Gusau a jihar Zamfara zuwa Shagamu a jihar Ogun lokacin da hatsarin ya afku.

    Guregi ya bayyana cewa mutane biyar sun mutu nan take, yayin da aka garzaya da waɗanda suka jikkata zuwa Asibitin Kwamishinan Agaie domin samun kulawa.

  4. Gwamnatin Najeriya za ta ci gaba da aikin kwaso ’yan Najeriya daga Afirka ta Kudu

    ....

    Asalin hoton, Getty Images

    Gwamnatin Najeriya ta tabbatar da cewa za ta ci gaba da kwaso ’yan ƙasar daga Afirka ta Kudu, inda ake samun fargabar hare-haren ƙyamar baƙi dab da zanga-zangar da ake shirin yi a ranar 30 ga Yuni.

    An ce wani jirgin Air Peace ya tashi daga Najeriya a ranar Litinin, tare da shirin kwaso wasu daga cikin ’yan ƙasar zuwa Legas a safiyar Talata.

    Kakakin ma’aikatar harkokin wajen Najeriya, Kimiebi Ebienfa, ya ce wannan mataki na daga cikin shirin gwamnati na ba da dama ga ’yan ƙasar da ke son dawowa gida cikin aminci.

    Wannan na zuwa ne yayin da ake ci gaba da shirin kwashe ’yan Najeriya kafin fara zanga-zangar adawa da baƙi a Afirka ta Kudu.

    Rahotanni sun nuna cewa fiye da ’yan Najeriya 700 na maƙale har yanzu a Afirka ta Kudu, kwanaki kaɗan kafin wa’adin da wasu ƙungiyoyin masu ƙyamar baƙi suka bayar ya cika.

    An kuma ce jinkirin fitar da kuɗin aikin kwaso ƴan ƙasar ya janyo tsaiko, lamarin da ya bar mutane da dama cikin barazana yayin da damuwar kai musu hare-hare ke ƙaruwa.

    Duk da haka, gwamnatin ta shawarci ’yan Najeriya da za su ci gaba da zama a Afirka ta Kudu su kasance cikin taka-tsantsan, su guji wuraren da ake zanga-zanga, tare da riƙa sadarwa da ofishin jakadancin Najeriya domin samun bayanai.

  5. Iran ta ƙara ƙaimi wajen yin kutse ta intanet tun bayan fara yaƙi - Isra'ila

    ....

    Asalin hoton, Getty Images

    Babban jami’in tsaron intanet na Isra’ila ya ce Iran ta ƙara ƙaimi wajen yin kutse ta intanet tun bayan fara yaƙi tsakanin ƙasashen biyu.

    Yossi Karadi ya bayyana cewa an samu ƙaruwa a kutsen intanet daga Iran a cikin watannin baya-bayan nan.

    A wata hira da ya yi da jaridar Die Welt ta Jamus, Karadi ya ce a watan Yunin 2025, lokacin da Isra’ila ke gudanar da hare-haren soji kan Iran, sun gano kusan kutse ta intanet daga Iran 1,600.

    Amma a cikin makonni huɗu na baya-bayan nan na Yunin 2026, adadin ya ƙaru zuwa kusan 4,800.

    Ya ƙara da cewa masu yin kusten daga Iran ƙwararru ne sosai inda ya kuma ce dole ne a ɗauki lamarin da muhimmanci.

    Karadi ya kuma ce kutsen da Iran take yi ta intanet ɗin na harin muhimman cibiyoyin ƙasa, da ƙananan da matsakaitan kamfanoni kamar na lauyoyi da masu binciken kuɗi, da kuma jama’a baki ɗaya.

  6. Hare-haren saman Pakistan a Afghanistan sun hallaka mutane da dama

    ....

    Asalin hoton, Getty Images

    Wani kakakin gwamnatin Taliban ya ce hare-haren sama da Pakistan ta kai kan yankuna a Afghanistan sun yi sanadiyyar kashe da jikkata fararen hula da dama, ciki har da mata da yara, a lardunan Paktika, Paktia da Kunar.

    Zabihullah Mujahid ya bayyana matakin na Pakistan a matsayin hari na “ban tsoro da ta’addanci,” yana mai cewa abin da ya faru ya saɓawa dokokin kasa da kasa ne.

    A wasu hotuna da aka wallafa a shafukan sada zumunta, an ga yara da fararen hula da suka jikkata sakamakon hare-haren.

    Sai dai a nata ɓangaren, Pakistan ta ce ta kai harin ne kan wuraren da ke karkashin mayaƙan Tehreek-e-Taliban Pakistan (TTP) da Jamaat-ul-Ahrar, inda ta ce ta kashe aƙalla mayaƙa 25.

    Jami’an Taliban sun ce aƙalla mutane 38 ne suka rasa rayukansu a hare-haren na daren jiya, inda mataimakin kakakin gwamnatin ya ƙara da cewa mutum 30 daga cikinsu sun mutu ne a kauyen Mandokhel da ke gundumar Samkani a lardin Paktia kadai.

  7. 'Iran da Amurka sun amince su rage tashin hankali da ci gaba da tattaunawa'

    ....

    Asalin hoton, Getty Images

    Wani jami’in gwamnatin Amurka ya bayyana cewa Iran da Amurka sun amince su dakatar da kai wa juna hare-hare tare da ci gaba da tattaunawa kan yarjejeniyar zaman lafiya.

    A cewarsa, za a ci gaba da tattaunawa kan dukkan fannoni na yarjejeniyar, yayin da ɓangarorin biyu za su ƙaurace wa ƙara tsananta rikici a halin yanzu, tare da bai wa jiragen ruwa damar zirga-zirga cikin ‘yanci.

    Duk da wannan bayani, har yanzu Iran ba ta tabbatar da rahoton ba.

    A ‘yan kwanakin nan dai, rikici ya ƙara tsananta sakamakon taƙaddama kan tafiyar da mashigar Hormuz, tare da kai wa juna hare-hare tsakanin Iran da Amurka, lamarin da ya ƙara yawan fargabar rushewar tsagaita wutar da ake ƙoƙarin cimmawa.

    Jami’in na Amurka, wanda ya nemi a sakaya sunansa, bai bayyana lokacin da kuma wurin da za a ci gaba da tattaunawar ba, sai dai wasu majiyoyi sun ce ana sa ran ɓangarorin biyu za su sake haɗuwa a Doha, babban birnin Qatar, domin ci gaba da tattaunawa, yayin da kowanne ɓangare ke zargin ɗayan da karya yarjejeniyar da aka cimma a baya-bayan nan.

  8. Za mu ɗauki tsauraran matakai kan duk wanda ya karya yarjejeniya - Iran

    ....

    Asalin hoton, Getty Images

    Ministan harkokin wajen Iran, Abbas Araqchi, ya yi gargaɗin cewa ƙasarsa za ta ɗauki tsauraran matakai kan duk wani ɓangare da ya karya yarjejeniyar da aka ƙulla, yana mai cewa irin wannan mataki na iya kawo cikas ga zaman lafiya da tsaron yankin.

    Araqchi, wanda ya kai ziyara ƙasar Iraki, ya bayyana hakan ne a yayin ganawarsa da Shugaban ƙasar, Nizar Amidi, inda ya ce karya wasu sashe-sashe na yarjejeniyar da Amurka da kuma Isra’ila suka yi musamman sashe na farko ya zama babban tarnaki ga ƙoƙarin dawo da kwanciyar hankali a yankin.

    Ya ƙara da cewa Iran na ƙoƙarin aiwatar da yarjejeniyar cikin gaskiya tare da bin ƙa’idar kowane ɓangare ya cika nauyin da ya rataya a kansa.

    Sai dai ya jaddada cewa Iran ba za ta lamunci duk wani saba yarjejeniyar ba, yana mai nanata cewa za su ɗauki matakan da suka dace domin kare muradun ƙasarsu da kuma tabbatar da dorewar zaman lafiya a yankin.

    Haka kuma, ya yi kira ga sauran ɓangarorin da ke cikin yarjejeniyar da su mutunta alƙawurran da suka ɗauka, yana mai cewa haɗin gwiwa da gaskiya su ne ginshikin warware rikice-rikice da ke addabar yankin Gabas ta Tsakiya.

  9. Assalamu alaikum

    ....

    Asalin hoton, Getty Images

    Jama'a barkanmu da wannan safiya ta Litinin daga wannan shafin namu na BBC Hausa, inda za mu ci gaba da kawo muku labaran kai-tsaye na abubuwan da suke faruwa a Najeriya da sassan duniya.

    Aisha Babangida ce ke fatan sake kasancewa da ku a daidai wannan lokaci.

    Za kuma ku iya leƙawa shafukanmu na sada zumunta na facebook da X da kuma whatsapp domin karanta wasu labaran da kallon bidiyo da ma tafka muhawara.

    Ku kasance tare da mu.