Ba mu yanke zuwa tattaunawa a Pakistan ba - Iran

Asalin hoton, Getty Images
Har kawo yanzu ƙasar Iran ta ce ba ta kammala yanke shawara ba dangane da ko za ta aika wakilai zuwa tattaunawar da za a yi da Amurka a Pakistan ba.
Mai magana da yawun ma'aikatar harkokin gida ta Iran ɗin, Esmail Baghei ya shaida cewa "ya zuwa yanzu...ba mu da wani shiri na zango na biyu na tattaunawa."
ShugabaTrump dai ya ce zai aika tawagar Amurka zuwa Pakista inda kuma mataimakin shugaban ƙasar, JD Vance zai jagoranta.
Bayanai sun nuna cewa tuni tawagar ta Amurka ta kama hanya zuwa Pakistan domin halartar tattaunawar.









