Abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya 31/07/2026

Wannan shafi ne da ke kawo muku abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya na ranar Juma'a 31 ga watan Yulin 2026.

Taƙaitattu

Tsallake Bidiyo ka ci gaba
  • Khalifa Dokaji
  • Sheikh Jingir
  • Kano
  • Seriki Abbas
  • xxx
  • xxx
  • Bola Tinubu
  • Senator Gaya
  • xxx
  • xxx
  • Zahra Buhari
  • xxx
  • Nigeria
  • xxx
  • Davido

Rahoto kai-tsaye

Haruna Kakangi, Isiyaku Muhammed da Abdullahi Bello

  1. Gwamnatin Najeriya ta ce ba ta da shirin ƙara kuɗin wutar lantarki

    Ministan Lantarkin ƙasar Joseph Tegbe

    Asalin hoton, @JosephOTegbe/X

    Gwamnatin Najeriya ta ce ba ta da wani shiri na ƙara kuɗin wuta lantarki a halin yanzu.

    Wata sanarwa da Bayo Onanuga ya fitar ta ambato Ministan Lantarkin ƙasar Joseph Tegbe na cewa abin da gwamnatin ta fi bai wa muhimmanci shi ne inganta samar da wutar lantarki, amfani da mitoci da kuma tabbatar da cewa ƴan Najeriya suna biyan kuɗin wutar da suka yi amfani da ita.

    Kalaman nasa sun zo ne bayan damuwar da ake ci gaba da nunawa kan tsadar kuɗin lantarki, musamman bayan sauye-sauyen farashi da aka yi a baya ga masu amfani da wutar Band A.

    Sai dai ministan ya ce gwamnati ba ta da wata manufa ta ƙara kuɗin lantarki fiye da yadda yake a yanzu.

    "Burinmu shi ne inganta wutar lantarki, tabbatar da kowa ya samu mita, sannan 'yan Najeriya su riƙa biyan kuɗin wutar da suka yi amfani da ita," in ji ministan.

    Ya ce gwamnatin tarayya za ta ci gaba da nazarin ƙarin hanyoyin da za su kare masu amfani da lantarki a wuraren da ba a cika samu ba da sauran matakai..

  2. Jami'ar ABU za ta fara yin digiri kan gudanar da aikin Hajji

    Hajj

    Asalin hoton, Getty Images

    Jami'ar Ahmadu Bello da ke Zaria ta rattaba hannu kan yarjejeniyar da Hukumar Alhazai ta Najeriya (NAHCON) domin fara koyar da digirin na biyu (MBA) a fannin gudanar da ayyukan Hajji.

    A wata sanarwa da NAHCON ta fitar, ta ce an sanya hannu kan yarjejeniyar ne a ranar Juma'a 31 ga Yulin 2026 a hedkwatar hukumar da ke Abuja.

    Shugaban hukumar NAHCON Ambasada Ismail Abba Yusuf ya bayyana cewa wannan matakin wani bababn ci gaba ne da zai bunƙasa yadda ake gudanar da harkokin Hajji da Umrah a Najeriya.

    "Gudanar da aikin Hajji na ƙara zama abu mai sarkakiya, hakan na buƙatar ƙwararrun ma'aikata masu ilimi, ƙwarewa da fahimtar yadda aikin Hajji ke sauyawa," in ji shugaban NAHCON

    NAHCON

    Asalin hoton, NAHCON

    Bayanan hoto, Shugaban NAHCON Ambasada Ismail Abba Yusuf, da Sakataren Hukumar, Dakta Mustapha Muhammad Ali, ne suka sanya hannu a madadin NAHCON. Shugaban ABU, Farfesa Adamu Ahmed, tare da Magatakardar jami'ar, Malam Rabiu Samaila, su ma sun rattaba hannu kan yarjejeniyar.

    Shugaban Jami'ar ABU, Farfesa Adamu Ahmed, ya ce wannan shiri ya samo asali ne bayan shafe kusan shekara goma ana tattaunawa da haɗin gwiwa tsakanin jami'ar da NAHCON.

    Za a gudanar da shirin digirin ta hanyar tsarin karatu daga gida.

    Za kuma a buɗe shirin ga jami'an NAHCON, hukumomin jin daɗin alhazai na jihohi, kamfanonin Hajji da Umrah masu lasisi, masu aikin sufuri, yawon buɗe ido da otal-otal, malamai, 'yan kasuwa da kuma waɗanda suka kammala jami'a da ke son yin aiki a fannin gudanar da aikin Hajji a Najeriya da ma ƙasashen duniya.

    "Wannan shi ne karon farko da irin wannan shiri zai taimaka wajen inganta ƙwarewa da ayyukan da ake yi wa alhazai, tare da mayar da Najeriya cibiyar ƙwarewa ta duniya a fannin ilimi," in ji NAHCON.

  3. Ghana ta amince da ƙudirin tsawaita wa'adin shugaban ƙasa zuwa shekara biyar

    Ghana ta amince da ƙudirin tsawaita wa'adin shugaban ƙasa zuwa shekara biyar

    Asalin hoton, Getty Images

    Gwamnatin Ghana ta amince da ɗaya daga cikin muhimman shawarwarin kwamitin gyara kundin tsarin mulkin ƙasar, wanda ya tanadi ƙara wa'adin mulkin shugaban ƙasa daga shekara huɗu zuwa biyar.

    Haka kuma gwamnatin ta amince da shawarar rage mafi ƙarancin shekarun da ake buƙata domin mutum ya tsaya takarar shugaban ƙasa daga shekara 40 zuwa 35.

    Waɗannan na daga cikin shawarwarin da kwamitin gyaran kundin tsarin mulkin ƙasar ya gabatar, yayin da Ghana ke ƙoƙarin yin gyaran kundin tsarin mulkinta na shekarar 1992.

    A ranar 19 ga Janairu, Shugaba John Mahama ya naɗa mutum takwas domin jagorantar kwamitin da zai sake nazarin kundin tsarin mulkin ƙasar.

    Kwamitin ya haɗa da wakilan ƙungiyoyin fararen hula, tsohon alƙalin Kotun Ƙoli, lauyoyi da kuma ƙwararru kan harkokin shugabanci.

    Kwamitin ya miƙa rahotonsa ga shugaban ƙasa a ranar 22 ga Disamban 2025.

    Shawarwarin sun shafi bangarori da dama na gwamnati, ciki har da bangaren zartarwa, majalisa, shari'a, kafafen yaɗa labarai da sauran fannoni na shugabanci.

  4. Trump ya ce ƙarfin sojin Iran ya yi rauni sosai

    Shugaban Amurka Donald Trump

    Asalin hoton, Reuters

    Shugaban Amurka Donald Trump ya jaddada buƙatar zamanantar da rundunar sojin ƙasar tare da ƙara zuba jari a harkokin tsaro.

    Trump ya sake yin ikirarin cewa an lalata ƙarfin sojin Iran na sama da na ruwa, yana mai cewa ƙarfin ƙasar wajen kera makamai masu linzami da jirage marasa matuƙa ya yi matuƙar raguwa.

    "Ƙarfinsu na kera makamai masu linzami da jirage marasa matuƙa da sauran makamai kusan ya ƙare," in ji Trump.

    A wani taron majalisar ministocinsa da Camp David, ya ce halin da sojojin Iran ke ciki a yanzu "mai matuƙar muni ne", kuma hare-haren da aka kai sun raunana manyan sassan ƙarfin sojin ƙasar.

  5. Kuwait ta ce ta lalata jirage marasa matuƙa daga Iran

    Sojojin Kuwait sun ce sun tarwatsa wasu jirage marasa matuƙa da suka shiga sararin samaniyar ƙasar da safiyar Alhamis.

    A wata sanarwa da rundunar sojin ƙasar ta wallafa a shafinta na X, ta ce faɗuwar ɓaraguzan jiragen ta jawo lalacewar wasu kayayyaki, amma ba a samu asarar rai ko jikkata kowa ba.

    Rundunar ta kuma zargi Iran da kai hari, tana mai cewa an kai farmaki kan wasu muhimman cibiyoyin sojinta a abin da ta bayyana a matsayin "hari daga Iran."

  6. Ƙungiyar HRW ta zargi sojojin Rasha da kashe fararen hula 8 a Mali

    Human Rights Watch ta zargi rundunar Africa Corps ta Rasha da kashe fararen hula a Mali

    Ƙungiyar kare haƙƙin bil'adama ta Human Rights Watch ta zargi rundunar sojin Rasha a Afirka ta Africa Corps da kai hare-hare ta sama sau biyu a yayin wani samamen soji da aka gudanar a tsakiyar ƙasar Mali a watan Yuni,

    Ƙungiyar ta ce hare-haren sun yi sanadin mutuwar fararen hula takwas, ciki har da yara uku.

    Ƙungiyar mai hedikwata a birnin New York ta buƙaci gwamnatocin Mali da Rasha su gudanar da bincike kan lamarin.

    Zarge-zargen na iya ƙara jawo damuwa game da faɗaɗar ayyukan rundunar sojin Rasha a yankin Sahel, inda ƙasashen Mali, Burkina Faso da Jamhuriyar Nijar suka juya baya ga ƙawayensu na Yamma tare da ƙara kusanci da Moscow domin neman taimako wajen yaƙi da ƙungiyoyin masu iƙirarin jihadi.

    Sai dai jami'an gwamnatocin Bamako da Moscow na ci gaba da musanta zarge-zargen da ke cewa hare-haren nasu na haddasa mutuwar fararen hula.

  7. Mene ne matsayin auren mutu'a?

    Auren Mutu'a, muhawarar kenan da ake tafkawa a arewacin Najeriya, kan halasci ko rashin halascinsa.

    Abin ya faro ne da bidiyon limamin Babban Masallacin Ƙasa a Najeriya, Farfesa Ibrahim Maƙari yana bayani kan wata tambaya daga ɗalibansa da ke zaune a ƙasashen waje.

    Bayanan bidiyo, Latsa hoton da ke sama domin kallon bidiyo
  8. 'Biyan bashi ne ke laƙume kuɗin Najeriya da aka tara bayan janye tallafi'

    Bola

    Asalin hoton, Getty Images

    Ministan kuɗin Najeriya ya ce kuɗaɗen da aka samu daga cire tallafin man fetur da kuma gyaran tsarin kuɗaɗen ƙasashen waje sun fi karkata wajen biyan bashin gwamnati da kuma ɗawainiyar gudanar da gwamnati da ya ya ƙaru.

    Wannan na zuwa ne a daidai lokacin da hukumomi a ƙasar ke ƙoƙarin kare sauye-sauyen tattalin arzikin da ake zargin sun ƙara tsananta rayuwar al'umma.

    Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya aiwatar da waɗannan sauye-sauye a shekarar 2023, lamarin da ya samu goyon bayan masu zuba jari da cibiyoyin ba da lamuni na duniya.

    Sai dai kuma sauye-sauyen sun haifar da tashin gwauron zabi na farashin kayayyaki da tsadar rayuwa ga miliyoyin ƴan Najeriya, abin da ya sa ake tambayoyi kan yadda aka yi amfani da kuɗaɗen da aka ce an tanada bayan cire tallafin.

    Da yake jawabi a taron African Emerging Markets Forum da aka gudanar a Abuja, Ministan Kuɗi, Taiwo Oyedele, ya ce kafin cire tallafin, tallafin man fetur da abin da ya bayyana da wani na tallafin kuɗaɗen waje sun kasance suna cin kusan kashi biyar cikin ɗari na kuɗaɗen da ake samu a cikin ƙasar.

    Oyedele ya ce wani ɓangare na kuɗaɗen da aka samu bayan cire tallafin na tafiya ne wajen biyan bashin gwamnati, saboda kuɗin ruwa na lamuni ya ƙaru daga kusan kashi 8% zuwa har kashi 24% bayan aiwatar da sauye-sauyen.

    Ya kuma ce albashin ma'aikatan gwamnati ya kusan ninka sau biyu, bayan da gwamnati ta ƙara mafi ƙarancin albashi daga baya zuwa naira 70,000 a wata.

    Ministan ya ƙara da cewa gwamnati ta ƙara kashe kuɗi kan shirin ba da rancen ilimi, wanda ke biyan kuɗin makaranta tare da ba ɗalibai fiye da miliyan 1.5 tallafin kuɗin rayuwa na wata-wata.

    Oyedele ya yi watsi da rahoton Asusun Ba da Lamuni na Duniya (IMF) wanda ya ce miliyoyin 'yan Najeriya na ci gaba da rayuwa cikin talauci duk da sauye-sauyen tattalin arzikin. Ya ce raguwar ƙarfin sayen kuɗin jama'a na ɗan lokaci abu ne da ba za a guje masa ba bayan cire tallafin.

  9. Shugaban ƙaramar hukumar da ya koma sana'ar ɗinki a Kano

    Tsohon Shugaban Ƙaramar Hukumar Kumbotso a Kano, Abdullahi Ghali (Basaf) ya ce ci gaba da sana'ar ɗinki tamkar yin rayuwarsa ce ta yau da kullum.

    Comrade Basaf, ya ce ya koma sana'ar ɗinkin ne don nuna wa jama'a cewa siyasa bai kamata ta zama hanyar rayuwa ta dindindin ba.

    Bidiyo - Abba Auwalu/Zahraddeen Lawan

    Bayanan bidiyo, Latsa hoton da ke sama domin kallon bidiyo
  10. An yi garkuwa da ɗan Jamus a Jamhuriyar Nijar

    Nijer

    Asalin hoton, ORTN

    Rahotanni sun ce wasu mayaƙan da ake zargin suna da alaƙa da ƙungiyar Islamic State in the Greater Sahara (ISGS) sun yi garkuwa da wani ɗan ƙasar Jamus wanda ɗan asalin asalin Turkiyya ne a yankin Tahoua da ke tsakiyar Jamhuriyar Nijar.

    Lamarin ya sake nuna cewa ƙungiyar na ci gaba da kasancewa a yankin, kamar yadda shafin Points Chauds mai zaman kansa ya ruwaito a ranar 30 ga Yuli.

    Rahoton ya ce mutumin ya isa birnin Niamey ne daga Algiers, kafin ya tafi yankin Tahoua domin harkokin kasuwancin zinariya. A hanyarsa ne ake zargin mayaƙan ISGS suka tare shi suka yi garkuwa da shi.

    Rahoton ya ƙara da cewa: "Daga baya, masu garkuwar sun tuntuɓi iyalansa domin tabbatar musu cewa suna tsare da shi."

    Wannan garkuwa da mutumin ta faru ne duk da ci gaba da hare-haren soji da gwamnatin Nijar tare da ƙawayenta na ƙawancen ƙasashen Sahel (AES) ke yi domin ƙwato yankunan da ƙungiyoyin masu iƙirarin jihadi suka mamaye.

    Sai dai har yanzu matsalar tsaro na ci gaba da tsananta a sassa da dama na ƙasar, musamman yankunan kan iyaka, inda ƙungiyoyin masu ɗauke da makamai ke ci gaba da gudanar da ayyukansu cikin sauƙi.

    Yankin Tahoua, wanda ke da muhimmanci ta fuskar kasuwanci da haƙar ma'adinai, ya zama ɗaya daga cikin wuraren da matsalar tsaro ta fi ƙamari a Nijar.

  11. Ghana ta amince da ƙudurin mayar da mulkin ƙasar shekara biyar

    Ghana

    Asalin hoton, Getty Images

    Gwamnatin Ghana ta amince da wasu muhimman gyare-gyare da kwamitin yi wa kundin mulkin ƙasar garambawul ya gabatar, ciki har da tsawaita wa'adin mulkin shugaban ƙasa da na 'yan majalisa daga shekara huɗu zuwa shekara biyar, kamar yadda kafafen yaɗa labarai na cikin ƙasar suka ruwaito a ranar 30 ga Yuli.

    Babban Lauyan Ƙasa kuma Ministan Shari'a, Dominic Aniye, ya ce: "Muna tunanin waɗannan zauye-zauyen za su yi. A ƙarƙashin tsarin wa'adin shekara huɗu na yanzu, watannin farko na kowane zangon mulki suna wucewa ne wajen karɓar mulki, sannan shekarar ƙarshe ta shige cikin shirye-shiryen zaɓe."

    Ya ƙara da cewa: "Wa'adin shekara biyar zai ba kowace gwamnati isasshen lokaci wajen tsara manufofi, aiwatar da su da kuma tantance sakamakonsu."

    Kwamitin ya miƙa rahotonsa na ƙarshe ga Shugaba John Mahama, inda ya ba da shawarar a yi wa kundin tsarin mulkin shekarar 1992 kwaskwarima.

    Gwamnatin ta kuma amince da wasu shawarwari da suka haɗa da:

    • Ƙara yawan kujerun majalisa daga 276 zuwa 300.
    • Rage mafi ƙarancin shekarun da ake buƙata domin tsayawa takarar shugaban ƙasa daga 40 zuwa 35.

    Sauran shawarwarin sun haɗa da:

    • Soke hukuncin kisa.
    • Taƙaita yawan ministoci zuwa 60 kacal.
    • Soke cikakken keɓewar shugaban ƙasa daga biyan haraji.
    • Taƙaita adadin alƙalan Kotun Ƙoli zuwa 19.
    • Samar da wa'adi guda ɗaya na shekara 10 ga Babban Alƙalin Ƙasa ba tare da damar sake naɗa shi ba.

    Ana sa ran za a gabatar da ƙudirin gyaran kundin tsarin mulkin nan da watan Oktoba, yayin da ake sa ran gudanar da ƙuri'ar raba gardama kan sauye-sauyen a shekarar 2027.

  12. 'Waɗanda suka sace ɗaliban Oyo sun buƙaci musaya da manyansu muka ƙi'

    Oyo

    Asalin hoton, Chukwunaeme Obiejesi

    Shugaban Najeriya, Bola Tinubu, ya ce gwamnati ta ƙi amincewa da buƙatun masu garkuwa da mutanen da suka kai hari makarantu uku a jihar Oyo da ke kudu maso yammacin ƙasar a ranar 15 ga Mayu.

    Maimakon haka, gwamnati ta mayar da hankali kan aikin ceto ɗaliban ne ta hanyar amfani da bayanan sirri, kamar yadda shafin jaridar Punch ya ruwaito a ranar 31 ga Yuli.

    Tinubu ya bayyana haka ne a karon farko tun bayan da aka ceto aƙalla ɗalibai da malamai 39 a ranar 10 ga Yuli, yayin wata ganawa da tawagar sarakunan gargajiya daga jihar Oyo a Abuja.

    Ya ce: "Mun ƙi tattaunawa kan biyan kuɗin fansa. Waɗannan masu aikata laifin sun buƙaci mu saki wasu daga cikin 'yan ƙungiyoyinsu da aka riga aka kama. Wannan na daga cikin sharuɗɗansu, baya ga kuɗin da suke nema."

    Ya ƙara da cewa: "Mun ce babu wata yarjejeniya. Ba za mu tattauna da masu aikata laifi ba. Sun aikata kisan kai, kuma mun shirya murƙushe su. Suna da iyalai da kuma al'ummomin da suka fito."

    Har ila yau, Tinubu ya danganta ƙaruwar sace-sacen mutane da hare-haren masu tayar da ƙayar baya a Najeriya da matsalolin tsaro da ke ƙasashen yankin Sahel.

  13. Mawaƙiyar Afirka ta Kudu Tyla ta fasa zuwa Najeriya taron kalankuwa

    Tyla

    Asalin hoton, Getty Images

    Mawaƙiyar Afirka ta Kudu, Tyla, ta cire Najeriya a cikin jerin ƙasashen da za ta je domin taron kalankuwa da ta shirya gudanarwa a ƙasashen duniya da dama.

    Ta shirya zuwa ƙasashen ne domin baje-kolin waƙoƙin sabon kundin waƙokinta.

    Sai dai alamu sun nuna ta fasa zuwa Najeriya bayan ce-ce-ku-ce da suka biyo bayan nuna wariyar baƙi a ƙasarta ta Afirka ta Kudu.

    A ranar Litinin ne Tyla ta sanar da ranakun rangadin , kuma a ciki ranaku uku na wasanni a nahiyar Afirka.

    Da farko dai an tsara za ta raƙashe ne a a Legas ranar 22 ga Disamba ne.

  14. Dubban baƙin-haure sun tsallaka Spain ta Morocco

    Baki

    Asalin hoton, Reuters

    Dubban ƙarin baƙin haure sun taru a kan bakin iyakar Ceuta, yankin Sifaniya da ke Arewacin Afirka, bayan da yankin ya fuskanci gagarumar kwararar masu shiga ƙasar a jiya Alhamis, karo na farko cikin shekara biyar.

    Gwamnatin Sifaniya ta tura karin sojoji domin taimakawa wajen shawo kan lamarin, yayin da ake sa ran Firaminista Pedro Sánchez zai kai ziyara yankin na Ceuta a yau Juma'a.

    Rahotanni sun ce hukumomin Maroko sun fara ɗaukar tsauraran matakai kan bakin hauren, inda a daren da ya gabata suka rika fesa wa bakin ruwa domin tarwatsa su.

    Spain

    Asalin hoton, EPA

    Sifaniya ta ce ta cimma yarjejeniya da Maroko domin mayar da bakin hauren zuwa ƙasarsu cikin gaggawa.

    Sai dai har yanzu babu wata sanarwa daga gwamnatin Maroko a kan batun. Jami'ai a Ceuta sun ce aƙalla mutum 15 sun mutu bayan da suka nutse a teku yayin da suke ƙoƙarin isa yankin na Sifaniya.

    Bayanan bidiyo, Latsa hoton da ke sama domin kallon bidiyo
  15. Kotu ta ba ƴansandan Brazil izinin binciken ɗan shugaban ƙasar

    Brazil

    Asalin hoton, Getty Images

    Wani alƙalin Kotun Koli ta Brazil ya bayar da izini ga ƴansanda su gudanar da binciken kan Fabio Lula da Silva, babban ɗan Shugaba Luiz Inácio Lula da Silva, bayan an danganta shi da wata badaƙalar zamba da ta shafi maƙudan kuɗaɗe.

    Ana zargin Fabio, wanda aka fi sani da Lulinha, da taimaka wa wani mai rajin neman tasiri a harkokin gwamnati da ke zaman kurkuku a yanzu, a mu'amalolinsa da Ma'aikatar Lafiya ta Brazil dangane da kasuwancin tabar wiwi da ake amfani da ita wajen magani.

    Mutumin da ake magana a kansa an same shi da laifin damfarar ƴan fansho a wata shari'a ta daban a bara, kuma tuni an taɓa binciken Lulinha dangane da wannan batu.

    Lauyoyin Fabio Lula da Silva sun shaida wa kafafen yaɗa labarai na Brazil cewa ba za su iya yin tsokaci kan sabon binciken ba, domin har yanzu ba su ga cikakkun bayanansa ba.

    Shugaba Lula ya sha alwashin cewa ba za a nuna sani ko sabo ba a kan dan nasa.

  16. Hamas ta amince ta ajiye makami a Gaza bayan tattaunawa da Trump

    Gaza

    Asalin hoton, Reuters

    Bayan tattaunawar wata da watanni, ƙungiyar Hamas ta ce ta amince da wani shiri da Hukumar Zaman Lafiya ta Shugaban Amurka Donald Trump ta gabatar, na ta kwance damarar yaki gaba daya - ta ajiye makamanta a Zirin Gaza.

    Trump ya bayyana yarjejeniyar a matsayin babban abin tarihi, yana mai cewa ta zama wani muhimmin mataki na samar da sabuwar gwamnatin Falasɗinawa a Gaza.

    Wakilin BBC a Gaza, wanda ke birnin Alkahira na Masar, ya ce shirin ya tanadi ƙididdige da adana manyan makaman Hamas da suka rage ƙarƙashin kulawar hukumomin Falasɗinawa.

    Wakiliyar BBC ta ce, zuwa yanzu Isra'ila ba ta ce komai ba. Shugaba Trump dai ya ce dakarun Isra'ila za su fice daga Gaza da zarar an kammala kwance damarar Hamas da sauran ƙungiyoyin da ke ɗauke da makamai.

  17. Masu bibiyar shafin labaran kai tsaye na BBC Hausa, barkanmu da safiyar wannan rana ta Juma'atu babbar rana.

    Kamar kodayaushe, za mu kawo maku labarai game da abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya.

    Za ku iya leƙawa shafukanmu na sada zumunta na facebook da X da kuma whatsapp domin karanta wasu labaran da kallon bidiyo da ma tafka muhawara.

    Ku kasance tare da mu.