Sabbin fuskokin masu horarwar da za a gani a Nahiyar Turai
Bayan kammala gasar Kofin Duniya da aka yi a Amurka da Mexico da kuma Canada, rashin nasarar da wasu ƙasashe suka yi na neman zama sanadin kawo sauye-sauye a tawagoginsu.
'Yan wasa da dama sun ajiye takalmansu kazalika masu horaswa. Amma wannan maƙalar za ta yi duba kan wasu ƙasashe da ke neman kawo sauyi a fannin horarwarsu.
Faransa:
Tun gabanin rashin nasarar da ta yi a kofin duniya ake yaɗa jita-jitan cewa za a sauya mai horarsa da tawagarta.
An ta cewa tsohon kocinta Zinedine Zidane zai maye gurbin kocinta na yanzu Didier Deschamp.
Amma bayan rashin nasarar da ta yi a hannun Spain managa ta ƙara ƙarfi, manyan jaridu turai ciki har da Fabrizio Romano sun rawaito cewa Zidane zai jagoranci Faransa har zuwa June 2030.
Wannan na nufin zai jagoranci ƙasar zuwa manyan gasar da suka haɗa da Nations League 2027 Euros 2028 da kuma Kofin duniya 2030.
Zidane ya yi wasa da Deschamp a 1998, tawagar da suka ci kofin duniya bayan doke Brazil 3-0.

Asalin hoton, Getty Images
Jurgen Klopp:
Bai zo da mamaki ba jin cewa Jurgen Klopp zai zama kocin Jamus na gaba ba, saboda daɗewa da ya yi ba tare da wata ƙungiya da yake jagoranta ba.
Babban abin da ya tabbatar da burinsa na jan ragamar Jamus shi ne tattaunawar da aka yi tsakanin Hukumar kwallon Kafa ta Jamus da tsohon kocin tawagar Julian Negelsman ya ce sun cimma matsaya da hukumar kan ajiye aikinsa.
Hukumar ta tabbatar da cewa Jurgen Klopp zai jagoranci Jamus sai dai ba a bayyana tsayin lokacin ba da kuma lokacin da zai fara aiki.
Tun daga 2014 da Jamus ta ci Kofin Duniya a hannun Argentina, Jamus ba ta ƙara cin wasa ba a mataki na sili daya kwale.

Asalin hoton, Getty Images
Pep Guardiola:
Aikin gaban Pep Guardiola zai zama babba ne, domin zai farfaɗo da tawagar da ake ganin ta zama mushen gizaga.
Hukumar kwallon ƙafa ta ITaliya ta aike da wakilai da suka haɗa da mai koyar da dabarun wasannin ƙasar wanda tsohon dan wasanta ne Paolo Maldini da mai bashi shawara Leonardo sun je har Barcelona sun tattauna da Guardiola na tsawon kwanaki uku.
Pep wanda ya yi nasara a zamansa a spain lokacin da ya jagoranci Barcelona da zamansa a Jamus inda ya yi kocin Beyern Munich sai kuma inda da ya horas da Manchester City, watakila Itali ta zama inda zai yi kocin na gaba.
Zai iya zama koci na biyu dan wata ƙasar da zai jagoranci Italiya kuma na farko tun shekarun1960.
Tsofaffin 'yan wasan ƙasar irinsu Roberto Mancini da Andrea Pirlo suma sun nuna shaawarsu kan aikin.
Guardiola mai shekara 55, aikin ba zai bashi wuya ba saboda yana jin yaren Italiya sosai, lokacin da ya zauna a ƙasar tsakanin shekarar 2001 zuwa 2003.

Asalin hoton, Getty Images
Mark van Bommel:
Mark van Bommel tsohon dan wasan Barcelona kuma ɗan asalin Netherland rahotanni na cewa zai karbi aikin horas da Belgium na tsawon shekara biyu zuwa watan Yunin 2028.
Belgium ma kamar sauran ƙasashen da suka fuskanci koma baya a gasar kofin Duniya ta kai matakin wasan kusa da dab da naƙarshe a gasar inda gwarzuwar gasar Spain ta doke ta da ci biyu da ɗaya.
Rudi Garcia wanda tsohon dan wasan Faransa ne shi ne ya kai Belgium kofin duniya, kuma ya kabi aikin ne a 2025.
Ana sa ran Van Bommel zai jagoranci tawagar zuwa shekarar 2028, bayan gasar Euro.

Asalin hoton, Getty Images


































