Mataimakin kocin Afirka ta Kudu ya samu bizar shiga Amurka ranar Talata, Gasar kofin duniya
Mataimakin kocin Afirka ta Kudu, Helman Mkhalele, ya samu bizar shiga Amurka ranar Talata, kuma zai tashi zuwa sansanin tawagar a Pachuca, Mexico, bayan da ƴan wasa da sauran ma’aikatan suka tafi gasar ba tare da shi ba a ranar Litinin.
Tafiyar Afirka ta Kudu zuwa gasar Kofin Duniya ta farko tun lokacin da suka karɓi bakunci a 2010 ta shiga rudani, bayan da aka gano cewa kuskuren gudanarwa ya sa yawancin ƴan wasa da ma’aikatan horarwa ba su samu bizar da ake buƙata ba a ranar da ya kamata su tashi da jirgin haya a ranar Lahadi.
Za su fara wasa da ƙasashen da ke karɓar bakunci, Mexico, a wasan buɗe gasar a Mexico City a ranar 11 ga watan Yuni, kuma sun rasa aƙalla rana guda na shiri da sabawa da yanayin Pachuca.
An fara ƙin amincewa da bukatar bizar Mkhalele da kuma Mdu Mbatha, daga Ofishin Jakadancin Amurka da ke Johannesburg saboda dalilan da ba a bayyana ba, amma yanzu an amince da su.
Shugaban hukumar ƙwallon ƙafa ta Afirka ta Kudu, Danny Jordaan, ya ce: “Zan tabbatar da cewa Helman da Mbatha sun samu bizar su, kuma za su tafi su haɗu da tawagar ranar Laraba duk za su kasance tare.”
Ya kuma ƙara da godiya ga ma’aikatan ofishin jakadancin Amurka.
Afirka ta Kudu za ta buga wasan sada zumunci da Jamaica a ranar Juma’a.
Suna cikin Rukunin A a gasar Kofin Duniya, inda bayan Mexico za su kara da Jamhuriyar Czech a Atlanta a ranar 18 ga watan Yuni, sannan su kara da Koriya ta Kudu a Monterrey kwanaki shida bayan nan.

Asalin hoton, Getty Images
















