Mun kama wanda ake zargi da harbi a wajen biki a Kano - Ƴansanda

Asalin hoton, Getty Images
Rundunar ’yansandan Kano ta ce ta kama wani mutum da ake zargi da harbin mutane a wajen bikin aure a Tudun Yola Bajallabe.
A cikin wata sanarwa da rundunar ta fitar a shafin sada zumuntarta na X, ta ce jami’anta sun gaggauta isa wurin bayan samun kiran neman agaji, inda suka kama wanda ake zargin tare da kwacd bindigar da aka yi amfani da ita wajen harbin.
Ta ƙara da cewa an garzaya da mutane huɗu da suka jikkata zuwa sakamakon harbin zuwa asibiti domin samun magani, sai dai likita ya tabbatar da mutuwar ɗaya daga cikinsu.
Rundunar ta ce sashen binciken manyan laifuka na SCID da ke Bompai na ci gaba da binciken lamarin.


















