Iran ta musanta harba wa Daular Larabawa makamai

Asalin hoton, TASNIM
Mai Magana da yawun ma’aikatar harkokin waje ta Iran ya musanta zargin da Haɗaɗɗiyar Daular Larabawa ta yi na cewa Iran ɗin ta harba mata makamai masu linzami.
Ismael Beqai ya bayyana a cikin wata sanarwa da ya fitar cewa “zargin na UAE ba shi da tushe balle makama”.
Mai Magana da yawun na Iran ya ce: “Matakin na Háɗaɗɗiyar Daular Larabawa ya saɓa da tsarin zama na maƙwaftaka kuma hakan zai iya yin cikas ga yunƙurin da ake yi na yayyafa wutar rikici tsakanin ƙasashen yankin.”
Sa’o’i bayan Iran ta sanar da cewa ta harba makamai ne ƙasar ta Haɗaɗɗiyar Daular Larabawa ta ce ta dakatar da duk wata alaƙa ta kasuwanci ko kuɗi da Iran har sai abin da hali ya yi.
Tun bayan ɓarkewar yaƙi tsakanin Iran da Amurka, Daular Larabawa ta kasance ƙasar da ta fi shan hare-hare daga Iran a yankin.


