Kana amfani da shafin BBC mai bayyana rubutu kawai (babu hoto) domin rage cin data. Idan ana so a ga hotuna da bidiyo sai a koma babban shafinmu.

Koma shafi mai hoto

Samu ƙarin bayani kan shafin tattalin data

KAI TSAYE, Abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya 10/06/2026

Wannan shafi ne da ke kawo muku abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya na ranar Laraba 6 ga watan Yunin 2026.

Rahoto kai-tsaye

Daga Aisha Babangida

  1. Pakistan ta kai hare-haren sama a Afghanistan

    Ƙasar Pakistan ta ƙaddamar da hare-haren sama masu muni a kan iyakarta da Afghanistan, lamarin da ya kawo ƙarshen zaman lafiya na watanni da aka samu a yankin da ke fama da rikici.

    Ministan yaɗa labaran Pakistan, Attaullah Tarar, ya bayyana a ranar Laraba cewa an lalata wurare hudu a wani hari da aka yi cikin tsari, wanda ya kashe ‘yan bindiga 26.

    Amma gwamnatin Taliban a Afghanistan ta ce hare-haren sun kashe mutane 13, ciki har da yara 11.

    Pakistan ta daɗe tana zargin Afghanistan da bai wa ‘yan ta’adda mafaka domin kai hare-hare a cikin ƙasarta, zargin da gwamnatin Taliban ke ci gaba da musantawa.

    Wannan sabon rikici shi ne na farko tun watan Fabrairu, lokacin da ƙazamin faɗa a kan iyaka ya yi sanadin mutuwar ɗaruruwan mutane.

    Ƙasashen biyu sun cimma yarjejeniyar tsagaita wuta a watan Oktoban bara bayan makonni na rikice-rikice masu muni.

    Attaullah Tarar ya ce hare-haren sun zo ne a matsayin martani ga “sabbin hare-haren ta’addanci a Pakistan,” inda aka kai farmaki kan wuraren ɓuya da horar da ‘yan bindiga, da kuma wuraren ajiye makamai a yankin iyaka.

    Tun bayan ƙazamin rikicin da ya faru a karshen watan Fabrairu, an samu arangama lokaci-lokaci, yayin da shugabannin duniya ke kira ga ƙasashen biyu da su dakatar da faɗa tare da rungumar zaman lafiya.

  2. Muna nazarin ci gaba da tattaunawa da Amurka bayan sabbin hare-hare - Iran

    Iran ta bayyana cewa za ta sake duba yiwuwar ci gaba da tattaunawa tsakanin ta da Amurka bayan sabbin hare-haren da aka ta kai.

    Mai magana da yawun ma’aikatar harkokin wajen Iran, Esmail Baghaei, ya bayyana hakan bayan sabuwar musayar wuta tsakanin ƙasashen biyu.

    Ya ce, “Harkar diflomasiyya ba ta gudana a cikin yanayi mara tasiri ba, domin ci gaba da kowace tattaunawa, dole ne a samu wani dan sarari da zai ba da damar ci gaba da aiwatar da ita.”

    Baghaei ya zargi Amurka da “lalata tsarin tattaunawar ta hanyar aika sakonni masu karo da juna da sauya matsaya akai-akai, da kuma karya yarjejeniyar tsagaita wuta sau da dama.”

    A safiyar ranar Laraba ne Amurka ta kai hare-haren sama a wasu wurare a kudancin Iran, a matsayin martani ga harbo jirgin yaƙinta da Iran ta yi a tekun Oman.

    A gefe guda kuma, sansanin Khatam al-Anbiya ya sanar da cewa sojojin juyin juya halin Iran sun kai hari a kan sansanonin Amurka da ke kasashen Bahrain, Kuwait da Jordan.

  3. 'Rukunin farko na 'yan Najeriya da aka kwashe daga Afirka ta Kudu zai isa ƙasar ranar Alhamis'

    Gwamnatin Najeriya ta ce ana sa ran rukunin farko na 'yan Najeriya da ake kwashe daga Afirka ta Kudu sakamakon hare-haren ƙyamar baƙi (xenophobia) za su isa ƙasar a safiyar ranar Alhamis.

    A wata sanarwa da kakakin Ma'aikatar Harkokin Wajen Najeriya, Kimiebi Ebienfa, ya fitar ranar Laraba, ya ce waɗanda za a kwashe za su tashi daga Afirka ta Kudu ne a daren Laraba.

    Ma'aikatar ta ce kamfanin jiragen sama na Air Peace ne zai gudanar da aikin jigilar mutanen, yayin da gwamnatin tarayya ta ɗauki nauyin dukkan kuɗaɗen aikin.

    Sanarwar ta tabbatar wa 'yan Najeriya cewa gwamnati, ta hannun ma'aikatu da hukumomin da abin ya shafa, ta shirya dukkan matakan karɓa da tallafa wa waɗanda za su dawo.

    Ya ce bayan isowarsu za a yi musu rijista da tantancewa tare da ba su tallafin da ya dace kafin a haɗa su da iyalansu.

    Tashin hankali ya ƙaru a Afirka ta Kudu bayan wata ƙungiya da ke adawa da baƙin haure marasa takardu ta buƙaci dukkan baƙi waɗanda ba su da izinin zama su fice daga ƙasar kafin ranar 30 ga Yuni.

    Kasashen Ghana da Mozambique sun riga sun kwashe ɗaruruwan 'yan ƙasarsu, yayin da Malawi da Najeriya suka sanar da shirinsu na yin hakan.

  4. 'Trump bai so ya sake kai wa Iran hari ba'

    Wasu jami’an gwamnatin Amurka sun ce shugaban ƙasar, Donald Trump, bai amince da buƙatar kai wa Iran harin ramuwar gayya ba sai da safiyar ranar Talata, kamar yadda ɗan jaridar Wall Street Journal, Alex Ward, ya ruwaito.

    A safiyar ranar Talata, Trump ya shaida wa Jaridar Wall Street Journal cewa harbo jirgin yaƙin Apache da Iran ta yi "ba wani babban al’amari ba ne", domin matuƙan jirgin sun tsira ba tare da sun samu raunuka ba.

    Sai dai rahoton ya ce daga baya shugaban ya sauya ra’ayinsa ne bayan Ministan Tsaron Amurka, Pete Hegseth, da shugaban rundunar hafsoshin tsaron ƙasa, Janar Dan Caine, sun ba shi shawarar ɗaukar matakin soja a wani taro da aka gudanar a Fadar White House.

    Daga ƙarshe, Trump ya amince da kai hare-hare kan wasu wurare a Iran a matsayin martani ga harbo jirgin yaƙin Apache, a cewar jami’an Amurka.

    Rahoton ya kuma ce bayan waɗannan hare-hare, rundunar juyin juya halin Iran da sojojin ƙasar sun ƙaddamar da sabbin hare-hare kan sansanonin sojojin Amurka da ke yankin.

  5. China ta buƙaci a rage tashin hankali a Gabas ta Tsakiya

    Ƙasar China ta bayyana matukar damuwa kan rikice-rikicen da ke faruwa a yankin Gabas ta Tsakiya, tana mai kira ga ƙasashen da abin ya shafa da su kauce wa ƙara dagula al’amura.

    Mai magana da yawun ma’aikatar harkokin wajen kasar, Lin Jian, ya ce ya kamata dukkan ɓangarorin su nuna haƙuri da kwantar da hankali, tare da ɗaukar matakai na gaskiya domin rage tashin hankali da gujewa faɗaɗa rikicin.

    Kiran na China ya zo ne bayan musayar hare-hare tsakanin Iran da Amurka, lamarin da ya ƙara tsananta damuwa a yankin baki daya.

  6. Iran ta kai harin makamai masu linzami kan sansanonin sojin Amurka uku

    Hukumomin labarai na Iran sun rawaito cewa rundunar juyin juya halin Musulunci (IRGC) ta kai hare-haren makamai masu linzami kan sansanonin sojojin Amurka guda uku da suka haɗa da Jordan da Bahrain da Kuwait.

    Iran dai ta harba aƙalla makamai masu linzami guda huɗu tare da wasu jirage marasa matuƙa da dama zuwa sansanonin sojojin Amurka ɗin.

    Wani jami'in Amurka ya tabbatar da harin, yayin da rahotanni suka ce an kai hare-haren ne a matsayin martani ga hare-haren da Amurka ta kai kan wasu wurare a Iran.

    A cewar IRGC, hare-haren sun kasance wani ɓangare ne na wata babbar martani inda suka yi iƙirarin kai hari kan wurare guda 21 na sojojin Amurka a yankin Gabas ta Tsakiya.

    Haka kuma rahotanni sun nuna cewa sojojin Jordan sun ce sun kakkabo wasu daga cikin makaman da aka harba, ba tare da rahoton asarar rayuka ko lalacewar dukiya ba.

    Kafofin yada labarai na Iran sun kuma wallafa wasu bidiyo da suka ce suna nuna lokacin harin da kuma fashewar da ta biyo baya, amma har yanzu ba a tabbatar da ingancin wadannan bidiyoyin ba daga kafafen labarai masu zaman kansu.

  7. Assalamu alaikum

    Jama'a barkanmu da wannan safiya ta Laraba daga wannan shafin namu na BBC Hausa, inda za mu ci gaba da kawo muku labaran kai-tsaye na abubuwan da suke faruwa a Najeriya da sassan duniya.

    Aisha Babangida ce za ta sake kasancewa da ku a daidai wannan lokaci.

    Za ku iya leƙawa shafukanmu na sada zumunta na facebook da X da kuma whatsapp domin karanta wasu labaran da kallon bidiyo da ma tafka muhawara.

    Ku kasance tare da mu.