Ƙudurin dokar neman ƙara yawan alƙalan kotu ya tsallake karatu na biyu a majalisa

Asalin hoton, Nigeria Senate
Ƙudurorin dokar da ke neman ƙara yawan alkalan manyan kotunan kasar sun tsallake karatu na biyu a Majalisar Dattawa domin rage cunkoso a harkar shari’a da kuma saurin yanke hukunci.
Ƙudurin ya buƙaci a ƙara yawan alƙalan Babbar Kotun Tarayya daga 70 zuwa 90, sannan a ƙara alkalai a kotun ɗaukaka ƙara daga 70 zuwa 110.
Shugaban masu rinjaye a majalisar, Sanata Opeyemi Bamidele, wanda ya gabatar da kudurorin, ya ce matakin zai ƙarfafa tsarin shari’a domin fuskantar ƙaruwar shari’o’i cikin sauƙi.
Ya ƙara da cewa dimokuradiyya ba za ta bunƙasa ba idan ba a samun hukunci cikin sauri, don haka dole a samar da isassun kayan aiki da ma’aikata ga ɓangaren shari’a.
Har ila yau, ƙudurin ya kuma tanadi daidaito wajen wakilcin jihohi da Babban Birnin Tarayya a kotun ɗaukaka ƙara, tare da inganta tsarin gudanarwa da aikin kotun.


















