Kana amfani da shafin BBC mai bayyana rubutu kawai (babu hoto) domin rage cin data. Idan ana so a ga hotuna da bidiyo sai a koma babban shafinmu.

Koma shafi mai hoto

Samu ƙarin bayani kan shafin tattalin data

KAI TSAYE, Abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya, Alhamis 16/07/2026

Wannan shafi ne da ke kawo muku labaran abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya, Alhamis 16/07/2026

Taƙaitattu

Rahoto kai-tsaye

Abdullahi Bello Diginza

  1. An dakatar da loda mai a tashar ruwan Iraki bayan wani hari ya faɗa kan tankar mai

    An dakatar da loda ɗanyen mai a tasoshin mai na Iraƙi bayan wani jirgi maras matuƙi ya bugi tankar mai

    Kamfanin dillancin labarai na Reuters ya ruwaito daga wasu majiyoyi tsaro da man fetur huɗu cewa an dakatar da loda ɗanyen mai a dukkan tashoshin man fetur na ƙasar a ranar Alhamis bayan wani harin jirgi maras matuƙi kan wata tankar mai a tashar man fetur ta Basra.

    Rahoton ya ce harin da jirgin maras matuƙin ya kai bai haddasa wata ɓarna ko tashin gobara ba.

    Tasoshin man fetur na Iraƙi suna kudancin ƙasar, kuma har yanzu ba a tabbatar da inda aka harbo jirgin marar matuƙin ba.

    Reuters ya ce hukumomin Iraƙi sun fitar da tankar man daga tashar ruwan tare da wata tankar mai ta daban a matsayin kariya.

    Kamfanin dillancin labarai na gwamnatin Iraƙi ya kuma ruwaito, ba tare da yin ƙarin bayani ba, cewa wani jirgi maras matuƙi ya faɗi a tashar ruwa ta Faw da ke Iraƙi a ranar Laraba, amma bai haddasa wata ɓarna ba.

  2. MDD ta nuna damuwa kan rahotonnin mutuwar ƴan Rohingya 500

    Majalisar Dinkin Duniya ta bayyana matuƙar damuwa game da rahotannin da ke cewa wasu jiragen ruwa biyu ɗauke da sama da mutum 500 ƴan ƙabilar Rohingya masu neman mafaka sun kife a kusa da gaɓar tekun ƙasar Myanmar.

    Jiragen ruwan sun tashi daga yammacin Myammar mako biyu da rabi da suka gabata, kuma tunda daga wannan lokacin ba a sake jin labarin mutanen 530 da ke cikin jiragen ba.

    Sama da 'yan ƙabilar Rohingya miliyan ɗaya ne ke zaune a sansanonin ƴan gudun hijira a ƙasar Bangladesh, bayan da sojojin Myanmar suka kora su daga ƙasar shekaru tara da suka gabata.

    Tsirarun musulman ƴan Rohingya sun samu kansu a tsakiyar yaƙin basasar Myanmar a birnin Rakhine, suna fuskantar wariya da tashin hankali da kai musu hare-hare, lamarin da ya tilasta wa wasu daga ciki tafiyar Hadari da tsallaka tekun Andaman domin tsallakawa kasar Malaysia.

    Kusan babu wata kafar da ake iya jin halin da ake ciki a jihar Rakhine, amma ƙungiyoyin kare hakkin dan adam sun ce an gano gawarwakin mutane da ruwa ya turo su a wurare biyu, da ake kyautata zaton na waɗanda ke cikin kwale-kwalen da ya nutse ne.

    Majalisar Dinkin Duniya ta ce ana bukatar samar da hanya ingantacciya domin ‘yan Rohinja da ke neman mafakar siyasa, sakamakon yadda ɗaruruwa ke mutuwa a teku, wasu kuma masu safarar mutane na cin zarafinsu.

    Sai dai babu wata kasa da ta nuna aniyar taimaka msu, ko saukaka hanyoyin da suke balaguron.

  3. Gobara ta kashe mutum 11 a cibiyar kula da yara ta Aljeriya

    Mutum 11 ne suka mutu sakamakon wata gobara da ta tashi a wata cibiyar kula da yara da ke Algiers, babban birnin ƙasar Aljeriya.

    Hukumar kare fararen ta ƙasar ta ce gobarar, wadda ta tashi da tsakar dare, ta kuma raunata mutum 19.

    Jami'an hukumar sun ce har yanzu suna aiki domin kammala daƙile wutar.

    Zuwa yanzu hukumar ba ta bayyana maƙasudin tashin gobarar ba.

    Aljeriya ta kwashe kwanaki tana fama da tsanann zafin rana, yayin da kamfanin dillancin labarai na AFP ya bayar da rahoton samun gobara fiye da 1,000 a ƙasar cikin mako guda.

    Hukumar kare muhalli ta ƙasar ta ce an samu rahotonnin gobarar daji 115 a cikin kwana guda.

    Shugaban ƙasar, Abdelmadjid Tebboune ya aike da saƙon jaje ga iyalan waɗanda lamarin ya shafa a cibiyar kula da ƙananan yaran, bayan mai bayyana lamarin da ''babban rashi''.

  4. Wasu daga cikin kadarorin Abubakar Malami da EFCC ta ƙwace

    A ranar Laraba ne wata babbar kotun tarayya da ke Abuja ta bayar da umanin ƙwace wasu kadarorin tsohon ministan sharia'ar Najeriya, Abubakar Malami

    Kotun ta ce ta bayar da umarnin ne saboda ta gano cewa ya mallaki kadarorin ne ba bisa ƙa'ida ba.

    EFCC ce dai ta shigar da ƙara ta buƙatar ƙwace kadarorin tsohon ministan guda 57 na dindindin da darajarsu ta kai naira biliyan 212.8.

    Abubakar Malami ya kasance ministan shari'ar Najeriya zamanin mulkin tsohon shugaban ƙasar, Muhammadu Buhari daga 2015 zuwa 2023.

  5. Jerin kadarori 48 da EFCC ta ƙwace daga Abubakar Malami

    A ranar Larabar nan ne wata babbar kotun tarayya da ke Abuja ta bayar da umarnin ƙwace kadarori masu alaƙa da tsohon ministan shari'ar zamani marigayi Muhammadu Buhari, Abubakar Malami, domin miƙa su ga gwamnatin tarayya.

    Da take yanke hukuncin, mai shari'a Joyce Abdulmalik ta ce hukumar EFCC ta riga ta tabbatar da cewa kadarorin da aka ƙwace an same su ne ba ta halastacciyar hanya ba.

    Kotun ta ara da cewa Malami ya gaza gamsar da ita cewa ya mallaki kadarorin nasa ne ta hanyar halaliya.

    Domin ganin kadarorin da aka ƙwacen karanta cikakken labarin a nan

  6. Iran ta ce ta kakkaɓo jirgin Amurka maras matuƙi

    Iran ta ce ta kakkaɓo jirgin Amurka maras matuƙi samfurin MQ-9, wanda ta ce yana shawagi a saman birnin Andimeshk.

    A cewar dakarun juyin juya halin ƙasar, an kakkaɓo da jirgin ta hanyar amfani da sabbin makamanta na tsaron sararin samaniya.

    Kamfanin dillancin labarai na Tasnim mai alaƙa da rundunar juyin juya halin ƙasar, ya ce aikin kakkaɓo da jirgin ya yi nasara, amma bai bayar da shaidar da za ta tabbatar da iƙirarin ba.

    Kawo yanzu gwamnatin Amurka da rundunar sojin ƙasar ta CENTCOM, ba su tabbatar da iƙirarin ba.

  7. Amurka da amince da sayar wa Saudiyya da Kuwait makamai

    Ma'aikatar harkokin wajen Amurka ta amince da sayar wa Saudiyya makamai na kusan dala biliyan 1.96 domin ƙarfafa tsarin kariyar sararin samaniyar ƙasar.

    Matakin na zuwa ne a daidai lokacin da rikice-rikice ke ƙara kamari a yankin Gabas ta Tsakiya.

    "Sayar da ya samu goyon bayan manufofin harkokin wajen Amurka da kuma muradun tsaronta ta hanyar ƙarfafa tsaron wata muhimmiyar ƙawa da ba mambar ƙungiyar NATO ba''.

    ''Saudiyya na taka muhimmiyar rawa wajen tabbatar da zaman lafiya da bunƙasar tattalin arziki a yankin Tekun Fasha." a cewar sanarwar ma'aikatar wajen Amurkan.

    Ma'aikatar ta kuma bayyana cewa yarjejeniyar sayar da makaman ta ƙunshi na'urorin sarrafa makamai masu linzami har 20,000, waɗanda za a yi amfani da su wajen hare-hare ta sama da ta ƙasa.

    Yarjejeniyar ta kuma haɗa da na'urorin harba makamai da bama-bamai da kayayyakin gyara da horaswa da kuma tallafin dabaru da sufuri.

    Haka kuma ma'aikatar harkokin wajen Amurkan ta amince da wani ƙunshin tallafi daban na dala miliyan 484 ga Kuwait domin tallafin fasaha ga jiragen sama.

    Ana sa ran kammala da aiwatar da waɗannan yarjejeniyoyin bayan majalisar dokokin Amurka ta yi nazari tare da amincewa da su.

  8. Mun kai hari kan sadarwar Amurka da tankokin mai a Jordan - Iran

    Kafofin yaɗa labaran Amurka sun ambato rundunar sojin ƙasar na cewa sun kai hari kan cibiyar sadarwar Amurka da wasu tankokin mai na sojojin Amurka a Jordan.

    Kamfanin dillancin labarai na Tasnim ya ce ''Iran ta yi amfani da jirage marasa matuƙa na yaƙi wajen ƙaddamar da hare-haren cikin dare a sansanin sojin Amurka na Al-Azraq da ke Jordan''.

    ''A wannan sansanin ne aka girke na'urorin kakkaɓo makaman linzami, kuma ana kallaonsa a matsayin ɗaya daga cikin cibiyoyi mafiya muhimmanci ga Amurka da yankin Yammacin Asiya'', kamar yadda Tasnim ya rubuta.

  9. Pakistan ta yi kira ga Iran da Amurka su koma teburin sulhu

    Ƙasar Pakistan ta ce ta yi kira ga Amurka da Iran su dakatar da yaƙin da ke tsakaninsu tare da komawa teburin tattaunawa domin gyara yarjejeniyar da aka cimma a watan da ya gabata.

    Kakakin ma'aikatar harkokin wajen Pakistan, Tahir Andrabi ya ce duk da ƙalubalen da aka samu wajen aiki da yarjejeniyar, Pakistan za ta ci gaba da ƙarfafa ɓangarorin biyu don kawo ƙarshen rikicin.

    ''Muna fatan halin da ake ciki kan mashigar Hormuz zai daidaita nan ba da jimawa ba''.

    Ya ƙara jaddada muhimmancin mashigar tare da ci gaba da tsareta da samar da ƴancin walwala ga jiragen da ke bi da wurin.

    A wannan makon ne Amurka da ƙaddamar da hare-hare kan Iran, yayin da ita ma tehran ta mayar da martani wajen kai wa sansanonin sojin Amurka hare-hare a yankin Gulf.

  10. 'An kashe wani babban injiniya Zaporizhzhia'

    Kamfanin makamashin nukiliya na gwamnatin Rasha ya ce an kashe babban injiniyan tashar samar da wutar lantarki ta nukiliya a yankin Zaporizhzhia, da ke Ukraine, wadda Rasha ke iko da ita, a harin da wani jirgin mara matuƙi na ƙasar Ukraine ya kai kusa da tashar.

    Hukumar Kula da Makamashin Nukiliya ta Duniya (IAEA) ta ce an sanar da ita game da mutuwar jami'in, tare da sake nanata kiranta da a dakatar da duk wani hari da ake kai wa kusa da cibiyoyin nukiliya da ma'aikatansu.

    Sojojin Rasha sun ƙwace iko da tashar Zapo-rijiya ne a makonnin farko na mamayar da Moscow ta ƙaddamar kan Ukraine a shekarar 2022.

    A wani labarin kuma, Rasha ta sake kai wa Kyiv babban birnin Ukraine, hare-haren makamai masu linzami , inda aka ba da rahoton fashe-fashe da dama a safiyar yau Alhamis.

  11. An ji ƙarar sabbin fashewa a Iran

    An ji ƙarar fashewar abubuwa a sassa daban-daban na Iran, ciki har da yankunan da ke nesa da Tekun Fasha, yayin da rundunar sojin Amurka ta sanar cewa ta ƙaddamar da wani sabon zagayen hare-hare.

    A babban birnin ƙasar, Tehran, an yi amfani da na'urar kakkaɓo makamai masu linzami yayin da a birnin Ah-vaz da ke kusa da arewacin Tekun Fasha.

    Kafafen yaɗa labaran ƙasar sun ce an kwashe marasa lafiya daga wani asibiti saboda hare-haren makamai masu linzami da aka kai a kusa da yankin.

    Babban mai shiga tsakani na Iran a tattaunawarta da Amurka, Mohammed Bagher Qalibaf, ya fitar da wata sanarwa yana mai cewa ƙasarsa na ci gaba da bin tafarkin tattaunawa da kuma yaƙi a lokaci guda, amma ya zama dole Iran ta ci gaba da riƙe ikon kula da mashigin ruwan Hormuz.

    Iran ta mayar da martani tana mai cewa ta mayar da hankali ne wajen lalata cibiyoyin sojin Amurka da ke yankin Gabas ta Tsakiya.

  12. Assalamu alaikum

    Masu bin shafin BBC Hausa barkanmu da safiyar wannan rana ta Alhamis.

    Abdullahi Bello Diginza ke fatan sake kasancewa da ku a daidai wannan lokacin domin kawo muku halin da duniya ke ciki.

    Ku biyo mu a shafukanmu na sada zumunta domin tafka muhawara kan labaran da muek wallafawa