Wasu daga cikin kadarorin Abubakar Malami da EFCC ta ƙwace

Asalin hoton, Facebook/EFCC
A ranar Laraba ne wata babbar kotun tarayya da ke Abuja ta bayar da umanin ƙwace wasu kadarorin tsohon ministan sharia'ar Najeriya, Abubakar Malami

Asalin hoton, EFCC/Facebook
Kotun ta ce ta bayar da umarnin ne saboda ta gano cewa ya mallaki kadarorin ne ba bisa ƙa'ida ba.

Asalin hoton, EFCC/Facebook
EFCC ce dai ta shigar da ƙara ta buƙatar ƙwace kadarorin tsohon ministan guda 57 na dindindin da darajarsu ta kai naira biliyan 212.8.

Asalin hoton, EFCC/Facebook
Abubakar Malami ya kasance ministan shari'ar Najeriya zamanin mulkin tsohon shugaban ƙasar, Muhammadu Buhari daga 2015 zuwa 2023.

Asalin hoton, EFCC/Facebook



















