Mu ke da iko da Mashigar Hormuz kuma dole a biya haraji - Iran
Mataimakin Kakakin Majalisar Dokokin Iran, Haji Babaei ya ce mashigar Hormuz ta kasance wurin da Tehran ba ta wasa da shi, kamar yadda kamfanin dillancin labarai na Mehrs mai alaƙa da dakarun juyin juya halin ƙasar ta ruwaito.
Ya ƙara da cewa Iran ce ke da cikakken iko da mashigar, kuma dole jirage su biya haraji kafin wucewa.
A ɗaya gefen kuma Shugaba Trump ya dage cewa za a buɗe mashigar ''nan ba da jimawa ba'', kamar yadda ya wallafa a shafinsa na sada zumunta.
Mataimakin Shugaban Amurka, JD Vance bai ambaci mashigar ta Hormuz ba a jawabin da ya yi wa manema bayan tattaunawar da suka ɗauki sa'o'i suna yi da wakilan Iran a Pakistan.
Muhimmiyar hanyar ruwan, wadda kashi 20 cikin 100 na man fetur da iskar gas na duniya ke bi ta wurin - na daga cikin sharuɗɗan tattaunawar.
Muhimmin sharaɗin da aka saka a tattaunawar shi ne wucewa ta mashigar lami lafiya.
Tun da farko rundunar sojin Amurka a Gabas ta Tsakiya ta ce jiragen sojinta biyu sun wuce ta mashigar a aranar Asabar, kodayake Iran ta musanta iƙirarin.
Rundunar juyin juya halin Iran ta yi gargaɗin kai hari kan duk jirgin sojin da ya yi yunƙurin wucewa ta mashigar.