Kana amfani da shafin BBC mai bayyana rubutu kawai (babu hoto) domin rage cin data. Idan ana so a ga hotuna da bidiyo sai a koma babban shafinmu.

Koma shafi mai hoto

Samu ƙarin bayani kan shafin tattalin data

KAI TSAYE, Yaƙin Iran da Amurka da Isra'ila da sauran abubuwan da ke faruwa a sassan duniya, Lahadi 12/04/2026

Wannan shafi ne da ke kawo muku labaran yaƙin Iran da Amurka da Isra'ila da sauran abubuwan da ke faruwa a sassan duniya, Lahadi 12/04/2026

Rahoto kai-tsaye

Daga Abdullahi Bello Diginza

  1. Mu ke da iko da Mashigar Hormuz kuma dole a biya haraji - Iran

    Mataimakin Kakakin Majalisar Dokokin Iran, Haji Babaei ya ce mashigar Hormuz ta kasance wurin da Tehran ba ta wasa da shi, kamar yadda kamfanin dillancin labarai na Mehrs mai alaƙa da dakarun juyin juya halin ƙasar ta ruwaito.

    Ya ƙara da cewa Iran ce ke da cikakken iko da mashigar, kuma dole jirage su biya haraji kafin wucewa.

    A ɗaya gefen kuma Shugaba Trump ya dage cewa za a buɗe mashigar ''nan ba da jimawa ba'', kamar yadda ya wallafa a shafinsa na sada zumunta.

    Mataimakin Shugaban Amurka, JD Vance bai ambaci mashigar ta Hormuz ba a jawabin da ya yi wa manema bayan tattaunawar da suka ɗauki sa'o'i suna yi da wakilan Iran a Pakistan.

    Muhimmiyar hanyar ruwan, wadda kashi 20 cikin 100 na man fetur da iskar gas na duniya ke bi ta wurin - na daga cikin sharuɗɗan tattaunawar.

    Muhimmin sharaɗin da aka saka a tattaunawar shi ne wucewa ta mashigar lami lafiya.

    Tun da farko rundunar sojin Amurka a Gabas ta Tsakiya ta ce jiragen sojinta biyu sun wuce ta mashigar a aranar Asabar, kodayake Iran ta musanta iƙirarin.

    Rundunar juyin juya halin Iran ta yi gargaɗin kai hari kan duk jirgin sojin da ya yi yunƙurin wucewa ta mashigar.

  2. Amurka ta kasa gamsar da wakilan Iran a tattaunawar Pakistan - Ghalibaf

    Kakakin majalisar dokokin Iran, Mohammad Bagher Ghalibaf - da ya jagoranci tawagar wakilan ƙasar a tattaunawar da aka yi a Pakistan - ya ce yanzu lokaci ya yi da Amurka za ta fahimci cewa ''za ta iya sayen imaninmu ko kuma a'a''.

    Cikin wani saƙo da ya wallafa a shafinsa na X, Ghalibaf ya jaddada maganar da ya yi kafin zaman, cewa Iran za ta je tattaunawar ne da ''zuciya ɗaya'', amma saboda abubuwan da suka faru a lokacin yaƙe-yaƙen ƙasar biyu da suka gabata, yanzu ''ba za ta yarda da abokan faɗanta ba''.

    Ya ce tawagar wakilan Iran ''ta nuna muradin cimma matsaya, amma ɗaya ɓangaren ya kasa gamsar da wakilan Iran a wannan tattaunawar''.

    Ghalibaf ya ci gaba da cewa: "Ba za mu yi wani abu da zai rusa nasarar da muka samu ta tsawo kwana 40 na kare ƙasarmu ba.''

    Ya ƙara da cewa sai da tattaunawar ta yi ''ƙarfi'', sannan ya gode wa Pakistan kan ƙoƙarinta na shirya zaman.

  3. Me ya sa Amurka da Iran suka kasa cimma matsaya?

    Wakilan Amurka da na Iran sun tashin baram-baran ba tare da cimma matsaya ba a tataunawar da suka a Pakistan da nufin kawo ƙarshen yaƙin da ƙasashen biyu ke gwambazawa.

    Tun da farko an cimma yarjejeniyar tsagaita wutar wucin gadi ta mako biyu bisa taimakon Pakistan, inda ƙasashen biyu suka amince da zama domin lalubo hanyoyin da za su kawo ƙarshen yaƙin.

    Ɓangarorin biyu sun gaatar da sharaɗɗan da suke ganin sai an amince da su kafin kawo ƙarshen yaƙin.

    Amurka, wadda ke samun goyon bayan Isra'ila a yaƙin ta gabatar da sharuɗɗa 15, yayin da Iran ta gabatar da 10.

    To sai dai ɓangarorin biyu ba su samu matsaya ba, lamarin da ya sa tattaunawa ta watse ba tare da wata matsaya ba.

    Kafofin watsa labaran Iran ɗin sun rawaito cewa buƙatun da Amurka ta gabatar da suka kira marasa kan gado ne suka hana samun ci gaba.

    Sun ce Amurka ta nemi Iran ta yi watsi da hatta haƙƙinta na samar da shirin nukiliya na farar hula don samar da magunguna da kuma wutar lantarki, wani abu Iran ɗin ta ce ya yi kama da yin saranda ko miƙa wuya.

    Wani abu da ya sake haifar da saɓanin shi ne batun matsayin mashigar Hormuz, da kuma batun tsagaita wuta a Lebanon.

  4. Trump ya halarci wasan kokawa a Miami

    A daidai lokacin da ake tattaunawar kawo ƙarshen yaƙin Amurka da Iran a Pakistan, Shugaba Trump ya halarci bikin kokawa a Miami tare da wasu daga cikin iyalansa da jami'an gwamnatinsa, ciki har da sakataren harkokin wajen ƙasar, Marco Rubio.

    Mataimakinsa, JD Vance - wanda ke jagorantar tawagar wakilan Amurka a Pakistan ya ce ya yi ta yin magana da Trump ''akai-akai'' ta waya a lokacin tattaunawar ta Pakistan.

    "Ban san sau nawa muka yi magana da shi ta waya ba, ko sau shida ne, ko sau 12 ne a cikin sa'a 21'', in ji Vance.

    Ya ƙara da cewa: ''Mun riƙa tuntuɓar jina a tawagar tamu, saboda mun je tattaunawar ce da zuciya ɗaya.''

  5. Iran ta yi gargaɗin kai hari kan duk jirgin sojin da ya yi yunƙurin shiga Hormuz

    Dakarun juyin juya halin Iran sun yi gargaɗin kai hari ga duk wani jirgin ruwa na soja da ya yi yunƙurin bi ta mashigin Hormuz.

    Kalaman sun zo ne bayan rundunar sojin Amurka a Gabas ta Tsakiya ta ce jiragen ruwan sojin Amurka biyu sun wuce ta mashigar, a karon farko tun bayan soma yaƙin.

    Sai dai Tehran ta musanta wannan iƙirari, tana mai cewa ita ce ke iko da mashigar ruwan.

    Tun da fari, Washington ta ce dakarunta sun fara cire nakiyoyi daga mashigar, ikirarin da Tehran ta sake musantawa.

    Wani jami’in sojan Amurka ya ce ƙoƙarin na mayar da hankali ne kan samar da hanya mai tsaro ga jiragen kasuwanci.

  6. Wakilan Iran sun kama hanyar barin Islamabad

    Tawagar wakilan Iran a tattaunawa da Amurka da aka yi a Pakistan ta kama hanyar komawa gida bayan gaza cimma yarjejeniya.

    Kamfanin dillancin labaran Iran Mehr ya ruwaito cewa wakilan ƙasar - ƙarƙashin jagorancin kakakin majalisar dokokin Iran, Mohammad-Bagher Ghalibaf - ta fice daga Pakistan da misalin ƙarfe 9:00 na safe agogon Pakistan.

    Ficewar tasu na zuwa ne jim kaɗan bayan tafiyar wakilan Amurka, bayan da tattaunawa tsakanin bangarorin biyu ta gaza.

  7. Wakilan Amurka na kan hanyar gida bayan gaza cimma matsaya a Pakistan

    Tawagar wakilan Amurka, ƙarƙashin jagorancin mataimakin shugaban ƙasar, JD Vance, na kan hanyarsa ta komawa Amurka bayan wata doguwar tattaunawa a birnin Islamabad na Pakistan da wakilan Iran ta gaza cimma yarjejeniya don kawo ƙarshen rikicin Gabas ta Tsakiya.

    Mista Vance ya bayyana tattaunawar a matsayin mai muhimmanci, amma ya ce ɓangaren Iran bai amince da abin da ya kira tayin ƙarshe na Amurka ba.

    Tawagarsa ta gaza shawo kan Iran, ta amince cewa ba za ta samar da makamin nukiliya, ko wasu kayayyaki da za su taimaka mata wajen ƙera makamin ba, wani batu da Iraniyawan suka sha musantawa.

    Kafofin watsa labaran Iran ɗin sun rawaito cewa buƙatun da Amurka ta gabatar da suka kira marasa kan gado ne suka hana samun ci gaba.

  8. Assalamu alaikum

    Masu bin shafin BBC Hausa kai-tsaye barkanmu da hutun ƙarshen mako.

    Abdullahi Bello Diginza ke fatan sake kasancewa da ku a daidai wannan lokaci domin kawo muku irin wainar da ake toyawa a faɗin duniya.

    Ku biyo mu a shafukanmu na sada zumunta domin tafka muhawara kan labaran da muke wallafawa.