Kana amfani da shafin BBC mai bayyana rubutu kawai (babu hoto) domin rage cin data. Idan ana so a ga hotuna da bidiyo sai a koma babban shafinmu.

Koma shafi mai hoto

Samu ƙarin bayani kan shafin tattalin data

KAI TSAYE, Abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya 21/8/2026

Wannan shafi ne da ke kawo muku muhimman abubuwan da ke faruwa a Najeriya da maƙwaftan ƙasashe da kuma sauran sassan duniya na ranar Juma'a 21 ga watan Agustan 2026.

Rahoto kai-tsaye

Abdullahi Bello, Haruna Kakangi

  1. Iyayen yara sun yi zanga-zanga a Borno

    Iyayen yaran da aka sace a jihar Borno da ke arewa maso yammacin Najeriya sun gudanar da zanga-zanga a garin Uba jiya Alhamis domin neman gwamnati ta ceto kusan yara 100 da ake garkuwa da su daga yankin.

    A ranar 15 ga watan Mayu ne wasu mahara da ake zargin mayaƙan Boko Haram ne suka kai farmaki a wata makaranta da ke ƙauyen Mussa mai maƙwaftaka da dajin Sambisa, inda suka sace ɗalibai kimanin 45 cikin har da ƙananan yara, wadanda har yanzu suke hannun ƴan bindiga.

    Zanga-zangar ta nuna yadda iyaye ke cikin damuwa kan yawaitar garkuwa da mutane da kuma hare-haren ƙungiyar Boko Haram duk da kasancewar sojoji a yankin.

    ISWAP da Boko Haram sun riƙa kai hare-hare da sace ɗalibai a makarantun yankin tsawon sama da shekara 15.

    Baya ga satar ɗaliban na ƙauyen Mussa, an kuma kai hari a wata makaranta a ƙauyen Lassa mai maƙwaftaka ranar 29 ga watan Yuni inda aka sace ɗalibai 36 da kuma malami waɗanda su ma har yanzu suna hannun masu garkuwa da su.

    A watan da ya gabata ne hukumomin ƙasar suka karɓo ɗalibai da malamai da aka yi garkuwa da su a jiyar Oyo da ke kudu maso yammacin ƙasar.

  2. Japan ta zartar da hukuncin kisa karo na farko cikin shekara ɗaya

    Japan ta aiwatar da hukuncin kisa na farko cikin sama da shekara guda.

    An yanke wa Sunayo Takami hukuncin kisa ne bayan samun shi da laifin kashe mutane biyar a wani hari da aka ƙona wani wurin wasa a shekarar 2009.

    Hakan na zuwa ne bayan shekaru 17 da aikata laifin, kuma shi ne na farko tun bayan zuwan wannan gwamnatin mai ci.

    Japan na daya daga cikin kasashe biyu kacal, wato ita da Amurka da ke cikin kungiyar G7 da ke aiwatar da hukuncin kisa, amma ba kasafai take aiwatar da shi ba.

  3. Barka da warhaka!

    Jama'a barkanmu da wannan safiya ta Juma'a a wannan shafin namu na BBC Hausa, inda muke kawo muku muhimman labarai kai-tsaye na abubuwan da ke faruwa a Najeriya, maƙwaftanta da kuma sassan duniya.

    Za ku iya leƙawa shafukanmu na sada zumunta na facebook, instagram da X da kuma whatsapp domin karanta wasu labaran da kallon bidiyo da ma tafka muhawara.

    Ku kasance tare da mu.