Kana amfani da shafin BBC mai bayyana rubutu kawai (babu hoto) domin rage cin data. Idan ana so a ga hotuna da bidiyo sai a koma babban shafinmu.

Koma shafi mai hoto

Samu ƙarin bayani kan shafin tattalin data

KAI TSAYE, Abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya 26/08/2026

Wannan shafi ne da ke kawo muku abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya na ranar Laraba 26 ga watan Agustan 2026.

Taƙaitattu

Rahoto kai-tsaye

Daga Aisha Babangida da Haruna Kakangi

  1. Me ya sa Atiku ya dage kan dawo da tallafin man fetur?

    Batun cire tallafin man fetur na ci gaba da haifar da muhawara a Najeriya gabanin babban zaɓen ƙasar na 2027.

    Babban ɗan takara na hamayya, Atiku Abubakar ne ya tayar da ƙurar lokacin da ya sanar cewa zai mayar da tallafin man fetur idan ya lashe zaɓen ƙasar na 2027.

    Kalaman na tsohon mataimakin shugaban ƙasar a makon da ya gabata sun ƙara zafafa siyasar ƙasar, lamarin da ya kai ga shugaban Najeriya Bola Tinubu da kansa ya fito ya soki lamirin kalaman na Atiku.

  2. Rikici a Sudan ya kashe mutum 27 ciki har da yara huɗu

    Aƙalla mutum 27 ne suka mutu, ciki har da yara huɗu, sakamakon sabon rikici da ya auku a jihar Kordofan ta Kudu da ke Sudan.

    Rahotanni sun ce hare-haren sun faru ne a yankunan Qardud da Abu Hamama, inda al'ummar Otoro ke zaune, yayin da wasu mata suka jikkata.

    Ƙungiyar likitocin Sudan ta zargi ƙungiyar 'yan tawayen SPLM-N ƙarƙashin jagorancin Abdel Aziz al-Hilu da kai hare-haren, tana mai cewa an kai wa fararen hula harin ne a yayin da rikici tsakanin ƙungiyar da al'ummar Otoro ke ƙara kamari.

    Ƙungiyar ta ce hare-haren sun haddasa ƙaura mai yawa zuwa yankunan Abu Hitan da Kadugli.

    Ta kuma yi gargaɗin cewa ci gaba da kai hari kan fararen hula bisa bambancin ƙabila na iya rikiɗewa zuwa wani babban rikicin ƙabilanci, tana mai bayyana hare-haren kan mata da yara marasa makami a matsayin karya dokokin jin ƙai na ƙasa da ƙasa.

  3. Iran ta ce har yanzu ba a yanke hukunci kan zaɓen ƙananan hukumomin ƙasar ba

    Ministan harkokin cikin gida na Iran, Eskandar Momeni, ya ce gudanar da zaɓen ƙananan hukumomi da na birane zai dogara ne da amincewar majalisar ƙoli ta tsaron ƙasa.

    Ya bayyana cewa tun da majalisar ce ta yanke shawarar ɗage zaɓen a baya, ita ce za ta sake yanke hukunci kan lokacin gudanar da shi.

    An shirya gudanar da zaɓen ne a ranar 1 ga watan Mayu, amma aka ɗage shi saboda damuwa cewa yanayin zaɓen na iya haifar da rarrabuwar kawuna da saɓani a lokacin da ƙasar ke fuskantar ƙalubale.

    Matakin ɗage zaɓen ya fuskanci suka daga wasu 'yan siyasa da tsoffin jami'ai.

    Shugaban Hukumar Sa-ido kan zaɓen majalisun ya ce an miƙa shawarar gudanar da zaɓen a ranar 14 ga Oktoba ga majalisar ƙolin domin ta yanke hukunci na ƙarshe.

  4. Ba za a iya cimma yarjejeniya ta hanyar diflomasiyya da Iran ba - Isra'ila

    Firaministan Isra'ila, Benjamin Netanyahu, ya bayyana cewa ba ya ganin za a iya cimma yarjejeniyar diflomasiyya da shugabannin Iran, yana mai cewa yana da shakku kan yiwuwar sasanta saɓanin da ke tsakanin Tehran da ƙasashen Yamma ta hanyar tattaunawa.

    Netanyahu ya faɗi hakan ne bayan ganawarsa da shugaban Amurka Donald Trump, inda ya ce sun tattauna yiwuwar samar da mafita ta diflomasiyya game da Iran.

    Sai dai ya jaddada cewa zai yi wahala a kai ga wata yarjejeniya da shugabannin Iran ta hanayr diflomasiyya.

    Kalaman nasa na zuwa ne a lokacin da ake ci gaba da yunƙurin diflomasiyya daga masu shiga tsakani, ciki har da Pakistan, domin rage zaman ɗar-ɗar da ke tsakanin Iran da Amurka da kuma nemo hanyar warware taƙaddamar ta hanyar tattaunawa.

  5. Hausawa na taka muhimmiyar rawa wajen haɗin kai da ci gaban Najeriya - Tinubu

    Shugaban Najeriya Bola Ahmed Tinubu ya ce Hausawa na taka muhimmiyar rawa wajen haɗin kai da ci gaban Najeriya, tare da yaba wa gudunmawar da al'ummar ke bayarwa wajen bunƙasa ƙasar.

    Tinubu ya faɗi hakan ne yayin da yake taya al'ummar Hausawa murnar ranar Hausa, wadda ake gudanarwa a masauratar Daura mai tarihi, cikin wani saƙo da ya wallafa a shafinsa na X.

    Ya ce harshen Hausa ya bunƙasa sosai, kuma ya zama wani muhimmin harshen sadarwa da kasuwanci a sassa daban-daban na duniya.

    Shugaban ya kuma taya ɗaukacin al'ummar Hausawa murna, yana mai yi musu fatan alheri yayin bikin ranar Hausa.

  6. Ƙarin ƴan Najeriya 65 za su koma gida daga Afirka ta Kudu a yau Laraba

    Gwamnatin Najeriya ta ce wasu ƙarin ƴan ƙasar 65 ne za su koma gida daga Afirka ta Kudu a yau Laraba, inda ake sa ran za su tashi daga filin jirgin OR Tambo da ke Johannesburg zuwa Legas.

    Ma'aikatar Harkokin Wajen Najeriya ta bayyana cewa wasu mutane masu zaman kansu ne suka ɗauki nauyin tafiyar, kuma ana sa ran jirgin zai tashi da misalin ƙarfe 3:30 na rana agogon Afirka ta Kudu, sannan ya isa filin jirgin Murtala Muhammed da ke Legas da yamma.

    Matakin na zuwa ne a yayin da ake ci gaba da nuna damuwa ƙyamar baƙi da hare-haren da ake kai musu da kuma tashin hankali da aka haifar musu a Afirka ta Kudu.

    A baya, gwamnatin Najeriya ta kwashe fiye da ƴan ƙasar 1,400 daga Afrika ta Kudu a lokutan da aka samu irin waɗannan rikice-rikice.

  7. Gobara ta hallaka jarirai 15 a asibiti a Pakistan

    Aƙalla jarirai 15 ne suka mutu bayan wata gobara ta tashi a wani asibiti da ke birnin Islamabad na Pakistan, inda ɗaya kacal daga cikin jariran da ke sashen kula da jarirai aka samu nasarar cetowa da ransa.

    Rahotannin kafafen yaɗa labarai na ƙasar sun ce gobarar ta tashi ne bayan na'urar sanyaya ɗaki ta fashe a sashen kula da mata masu juna biyu na Cibiyar Kimiyyar Kiwon Lafiya ta Pakistan (PIMS).

    Gobarar ta bazu zuwa sashen jarirai, lamarin da ya haddasa asarar rayuka masu yawa.

    Jami'ai sun ce an kashe gobarar, kuma jami'an agajin gaggawa na ci gaba da aikin sanyaya wurin da kuma tantance irin ɓarnar da gobarar ta yi.

    Hukumomi sun kuma fara bincike domin gano musabbabin aukuwar lamarin.

  8. Wace ce Dolly Parton, fitacciyar mawaƙiyar Amurka da ta rasu?

    Fitacciyar mawaƙiya, jaruma kuma marubuciyar waƙoƙi ta Amurka, Dolly Parton, ta rasu tana da shekara 80 a duniya.

    An haifi Dolly Rebecca Parton a ranar 19 ga Janairun 1946 a jihar Tennessee ta Amurka, inda ta taso cikin iyali mai yara 12.

    Tun tana ƙarama ta fara rubuta waƙoƙi kuma ta shiga harkar kiɗa, lamarin da ya sa daga baya ta zama ɗaya daga cikin fitattun mawaƙan waƙoƙin country a tarihin Amurka.

    Dolly Parton ta yi fice da waƙoƙi irin su Jolene, I Will Always Love You da kuma 9 to 5, waɗanda suka samu karɓuwa a faɗin duniya.

    Baya ga harkar waƙa, ta yi fice a fina-finai da dama, sannan ta kafa cibiyar nishaɗi ta Dollywood da kuma shirin Imagination Library, wanda ke raba littattafai kyauta ga yara domin ƙarfafa karatu.

    A tsawon aikinta, ta lashe lambobin yabo da dama ciki har da Grammy, kuma ta sayar da sama da kwafi miliyan 100 na ƙundin waƙoƙinta.

    Mutuwar Dolly Parton ta jawo alhini daga magoya bayanta da masu sha'awar kiɗa a duniya, inda ake yi mata kallon ɗaya daga cikin fitattun mata da suka canza fagen waƙoƙin country.

    Ba saboda nasarorin da ta samu a harkar nishaɗi kaɗai aka santa ba, har ma saboda ayyukan jin ƙai da tallafin da ta riƙa bayarwa ga yara da al'ummomi masu buƙata.

  9. Iƙirarin Amurka na cire nakiyoyi a mashigar Hormuz farfaganda ce - Iran

    Mataimakin ministan harkokin wajen Iran, Kazem Gharibabadi, ya yi watsi da ikirarin shugaban Amurka Donald Trump cewa an cire dukkan nakiyoyin da ke mashigar Hormuz, yana mai cewa wannan "ƙarya ce ta farfaganda".

    Ya ce idan har Amurka ta cire nakiyoyin kamar yadda take ikirari, me ya sa har yanzu babu jiragen ruwa da ke iya wucewa ta mashigar.

    Gharibabadi ya kuma yi barazanar cewa Iran za ta kai wa jiragen Amurka masu aikin gano da cire nakiyoyi za su zama hari idan suka shiga yankin.

    Kalaman nasa sun zo ne a daidai lokacin da Iran da Oman ke ci gaba da tattaunawa kan samar da wata hanya ta musamman domin zirga-zirgar jiragen kasuwanci a mashigar Hormuz.

    Jami'in na Iran ya ce ko da an kammala yarjejeniyar da ake tattaunawa da Oman, ba za a sake buɗe mashigar nan take ba.

    Ya bayyana cewa sabuwar hanyar za ta kasance ta wucin-gadi, inda jiragen ruwa za su riƙa shiga Tekun Fasha ta ruwan Iran sannan su fita ta ruwan Oman.

    Ya kuma ce idan cikin kwanaki 30 zuwa 60 ba a cimma matsaya kan wata yarjejeniya ta dindindin da za ta biya buƙatun Iran ba, to mashigar Hormuz za ta ci gaba da kasancewa a rufe.

  10. Shugabannin ƙasashen Iran da Rasha za su gana mako mai zuwa

    Jakadan Iran a Rasha, Kazem Jalali, ya ce shugaban Iran Masoud Pezzekiyan da takwaransa na Rasha Vladimir Putin za su gana a mako mai zuwa a gefen taron ƙungiyar haɗin gwiwar Shanghai (SCO) da za a gudanar a Bishkek, babban birnin Kyrgyzstan.

    Jalali ya bayyana cewa wannan ita ce ganawa ta shida tsakanin shugabannin biyu tun bayan da gwamnatin Masoud Pezzekiyan ta hau mulki.

  11. Assalamu alaikum

    Jama'a barkanmu da wannan safiya ta Laraba daga wannan shafin namu na BBC Hausa, inda za mu ci gaba da kawo muku labaran kai-tsaye na abubuwan da suke faruwa a Najeriya da sassan duniya.

    Aisha Babangida ce za tan kasance da ku a wannan lokaci.

    Za kuma ku iya leƙawa shafukanmu na sada zumunta na facebook da X da kuma whatsapp domin karanta wasu labaran da kallon bidiyo da ma tafka muhawara.

    Ku kasance tare da mu.