Rikicin Crystal Palace da Mateta na kara dagulewa
Sabon salo a rikicin da ke tsakanin Jean-Philippe Mateta da Crystal Palace, wanda a 'yan kwanakin nan ya kasance tamkar tafiyar jirgin ƙasa mai cike da sauye-sauye, ya sake jefa makomar ɗan wasan a kulob ɗin cikin tambaya.
Bayyanawar da BBC Sport ta yi ranar Asabar cewa Mateta na jayayya cewa shekarar ƙarshe da ke cikin kwantiraginsa da Palace ba ta da inganci, tare da matakin da ya ɗauka na kai ƙarar gaban wata kotun sulhu mai zaman kanta ta Premier League da kuma sauraron ƙara a Fifa, ya ƙara sanya lamarin ya zama mai jan hankali yayin da kasuwar saye da sayar da 'yan wasa ke gab da rufewa.
Duk da cewa Mateta da mashawartansa suna kalubalantar cewa shekarar ƙarshe da ke cikin yarjejeniyarsa ba ta da ɗaurewa a doka, saboda ƙarin shekarar wata zaɓi ce da kulob ɗin ya amince daga cikin ainihin kwantiraginsa na shekaru huɗu da rabi, har yanzu ɗan wasan na ƙasar Faransa yana ƙarƙashin kwantiragi da Crystal Palace.
Kwanaki kaɗan kafin ya fara wasan farko na Palace a Premier League da Everton, Fifa ta yanke hukunci cewa batun ba ya cikin huruminta.
Kuma ko da yake ba a bayyana sakamakon hukuncin kotun sulhu mai zaman kanta ta Premier League da aka yi a kakar wasan da ta gabata ba, kasancewar Mateta har yanzu yana ƙarƙashin kwantiragi da Palace na nuna cewa hukuncin bai zai yi masa dadi ba.