Kana amfani da shafin BBC mai bayyana rubutu kawai (babu hoto) domin rage cin data. Idan ana so a ga hotuna da bidiyo sai a koma babban shafinmu.

Koma shafi mai hoto

Samu ƙarin bayani kan shafin tattalin data

KAI TSAYE, Abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya 15/06/2026

Wannan shafi ne da ke kawo muku abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya na ranar Litinin 15 ga watan Yunin 2026.

Rahoto kai-tsaye

Daga Aisha Babangida da Usman MINJIBIR

  1. Sojojin Najeriya sun kama ƴan ƙasashen wajen 46 a wani aikin samar da tsaro

    Sojojin Najeriya sun sanar da kama ƴan ƙasashen waje 46 a wani aikin samar da tsaro da suka gudanar a jihar Ogun da ke yankin kudu maso yammacin ƙasar.

    A cewar rundunar, an kai samamen ne a ranar Alhamis a yankunan Ijebu Imushin da Ijebu Ilese tare da wasu ƙauyuka da ke kusa, bayan samun bayanan sirri masu muhimmanci.

    Mai magana da yawun rundunar, Idereghi Samuel Akari, ya ce binciken farko ya nuna cewa mutanen sun shafe kusan watanni shida a Najeriya ba tare da takardun izinin zama ba.

    Ya ƙara da cewa mutanen sun shaida wa jami’an bincike cewa su ‘yan kasuwa ne da ma’aikata masu alaƙa da kamfanin QNET, wani kamfanin sayar da kayayyaki ta intanet mai hedikwata a Hong Kong.

    Sai dai kamfanin QNET ya sha fuskantar zarge-zarge a Najeriya, inda hukumomi ke danganta kamfanin da damfara da safarar mutane da kuma shigo da mutane ba bisa ƙa’ida ba amma kuma kamfanin ya musanta hannu a irin waɗannan ayyuka, yana mai cewa yana nesanta kansa da masu amfani da sunansa wajen aikata laifi.

    Kamen na zuwa ne a daidai lokacin da ake ƙara nuna damuwa a yammacin Afirka kan wasu ƙungiyoyin da ake zargi da amfani da sunan kamfanin wajen yaudarar mutane da alƙawuran samun aiki a ƙasashen waje da kuma samun kuɗi cikin sauƙi.

    Daga cikin mutanen da aka kama, guda 18 ‘yan ƙasar Burkina Faso ne, 23 kuma daga Ivory Coast, huɗu daga Togo yayin da kuma mutum ɗaya daga Senegal ne.

    Daga bisani, an miƙa waɗanda aka kama ga Hukumar Shige da Fice ta Najeriya domin ci gaba da bincike.

  2. Za mu iya sayar da manmu ba tare da wata matsala ba - Iran

    Mai magana da yawun Ma’aikatar Harkokin Wajen Iran, Esmail Baghaei, ya bayyana cewa idan an sa hannu kan yarjejeniyar Iran da Amurka, Iran za ta fara sayar da man fetur da kayayyakin sinadarai da sauran kayayyakin mai ba tare da wata tangarda ba.

    Baghaei ya ce batun shirye-shiryen nukiliyar Iran bai shiga cikin yarjejeniyar ba, amma za a fara tattaunawa a kansa washegarin da aka kulla yarjejeniyar.

    Ya jaddada cewa har yanzu ba a tattauna cikakkun bayanai ba, amma matsayar Iran a kan shirin nukiliyarta a bayyane yake, inda ya ce:

    "Dage dukkan takunkumai, ciki har da na farko da na biyu, da na Kwamitin Tsaro na Majalisar Dinkin Duniya, da kuma wadanda suka shafi Hukumar IAEA na daga cikin batutuwan da za a tattauna washegari bayan sanya hannu, kuma ana sa ran a cimma matsaya cikin kwanaki 60."

    Har ila yau, ya bayyana cewa sakin kadarorin Iran da aka toshe a ketare, da kuma gyaran asarar tattalin arziki suna daga cikin muhimman batutuwa, yana mai cewa ɓangaren Amurka ya yi alkawarin ɗaukar matakai a wadannan fannoni.

    Baghaei ya ƙara da cewa yarjejeniyar ta kuma ƙunshi batun farfaɗo da asarar tattalin arzikin da Iran ta fuskanta.

  3. ADC ta zaɓi Amaechi a matsayin mataimakin Atiku

    Jam’iyyar haɗaka ta ADC ta zaɓi tsohon gwamnan jihar Rivers kuma tsohon ministan sufuri, Rotimi Amaechi, a matsayin ɗan takarar mataimakin shugaban ƙasa tare da Atiku Abubakar gabanin zaɓen 2027.

    Jam’iyyar ta bayyana haɗin nasu a matsayin “tikitin haɗin kai da ceto ƙasa.”

    Sakataren yaɗa labarai na ƙasa na jam’iyyar, Mallam Bolaji Abdullahi ne ya sanar da hakan a cikin wata sanarwa da ya fitar inda ya ce an zaɓi Amaechi ne bayan shawarwari masu zurfi da shugabannin jam’iyya da masu ruwa da tsaki.

    Ya ƙara da cewa Amaechi ya samu goyon baya sosai a zaɓen fidda gwani inda ya zo na biyu, kuma yana da ƙwarewa a harkokin gwamnati.

    Jam’iyyar ta ce gogewar Amaechi a fannoni daban-daban na sanya shi cikin sahun manyan ‘yan siyasa masu cikakken ƙwarewa.

    Ta ce wannan gogewa za ta taimaka wajen ƙarfafa jagorancin Atiku da kuma faɗaɗa tasirin jam’iyyar a faɗin ƙasar.

    ADC ta kuma bayyana cewa haɗin Atiku da Amaechi zai haɗa yankuna da al’umma daban-daban a Najeriya.

  4. Isra’ila ta soki yarjejeniyar Iran da Amurka, ta ce barazana ce ga tsaro

    Isra’ila ta soki yarjejeniyar fahimta da aka cimma tsakanin Iran da Amurka, tana mai cewa yarjejeniyar na iya zama barazana ga tsaronta da kuma zaman lafiyar yankin.

    Yayin da wasu ƙasashe suke maraba da yarjejeniyar, jami’an gwamnatin Isra’ila sun bayyana rashin amincewarsu da ita, suna masu cewa ba za ta magance barazanar da suke ganin Iran ke haifarwa ba.

    Amma kuma firaministan Isra’ila Benjamin Netanyahu bai fito da martani a hukumance ba.

    Ministan tsaron cikin gida, Itamar Ben-Gvir, ya ce Isra’ila ba ta da wani wajibi na bin yarjejeniyar, yana mai jaddada cewa ƙasar mai cin gashin kanta ce.

    Ya ƙara da cewa ba za su amince da duk wata yarjejeniya da ba ta tabbatar da tsaron Isra’ila ba, yana mai cewa dole ne a lalata Hezbollah gaba ɗaya kuma ba za su janye daga yankunan da suka ƙwace ba.

    Haka kuma Ministan kuɗi, Betzalel Smotrich, ya soki yarjejeniyar yana mai cewa ba ta da amfani ga Isra’ila da sauran ƙasashen duniya masu ‘yanci.

    Ya ce dole ne Isra’ila ta ci gaba da neman hanyoyin da za ta hana Iran mallakar makamin nukiliya tare da ƙoƙarin kifar da tsarin mulkin ƙasar.

  5. Sojoji sun ƙaddamar da wani gagarumin aikin soji a Katsina bayan mutuwar Janar Rabe

    Hedkwatar Tsaron Najeriya ta ƙaddamar da wani sabon gaggarumin aikin soji da ta yi wa laƙabi da Operation Clean Sweep III a ƙaramar hukumar Matazu da ke jihar Katsina domin yakar ƴan ta’adda da ƴanbindiga.

    An fara wannan gaggarumin aiki ne bayan mutuwar tsohon Manjo Janar Rabe Abubakar mai ritaya, wanda ya mutu a hannu yanbindigar da suka yi garkuwa da shi da matar shi.

    Hedkwatar ta ce dakarunta sun fara aikin ne a ranar 14 ga Yuni 2026, domin kamo waɗanda suka aikata laifin tare da rushe hanyoyin ayyukan su, da kuma dawo da tsaro a yankunan da abin ya shafa.

    Sojojin sun ce tun bayan ƙaddamar da aikin, sun gudanar da sintiri da kai hare-hare bisa bayanan sirri, da bincike a wuraren da ake zargin ƴan ta’adda na ɓoye.

    An binne marigayin Janar Rabe Abubakar a ranar Lahadi da misalin ƙarfe 6 na yamma a makabartar Gidan Dawa da ke cikin birnin Katsina.

    Rundunar ta kuma ce za su ci gaba da matsa lamba kan ƴan ta’adda har sai sun kammala manufar wannan aiki.

  6. Tambayoyi da ƙilawaƙala kan yarjejeniyar Iran da Amurka

    Sanarwar cimma yarjejeniyar kawo ƙarshen rikicin da ake yi tsakanin Amurka da Iran ta kasance wata kyauta ta musamman ga Donald Trump yayin da ya ke shirin yin bikin zagayowar ranar haihuwarsa - ko da yake dai rigar rashin tabbas ta ƙanannade yarjejeniyar.

    Shugaban na Amurka ya wallafa a shafinsa na kafafen sada zumunta inda ya shelanta yarjejeniyar cewa za a buɗe mashigar Hormuz inda za a ci gaba da safarar jiragen ruwa na kasuwanci kuma Amurka za ta janye takunkumin da ta ƙaƙaba.

    "A Bari man fetur ya kwarara!" Trump ya furta a ranar Lahadi.

    Ya ci gaba da bayyana cewa, saɓanin gazawar shugabannin Amurka da suka shuɗe, ya yi nasarar ƙulla "muhimmiyar yarjejeniya" da za ta samar da "zaman lafiya da tsaro a yankin baki ɗaya".

    Irin wannan iƙirarin dai ba sabon abu ba ne ga Trump. Bugun ƙirjin da ya yi game da yarjejeniyar da aka cimma a bara da ta kawo ƙarshen yaƙin Gaza wadda ya bayyana a matsayin- "zaman lafiya da zai ɗore har abada" kuma "farkon zamanin samun aminci da imanin ga Allah" - duk da cewa dai lamarin da ke ƙasa ya sha bambam da kalaman na sa.

  7. Za a gurfanar da mutum 400 a gaban kotu kan zargin aikata laifukan ta'addanci

    Aƙalla mutum 400 ne za a gurfanar a gaban Kotun Tarayya da ke Abuja a ranar Litinin din nan kan zargin aikata laifukan ta’addanci, a ɗaya daga cikin manyan shari’o’in ta'addanci da aka taɓa yi a Najeriya.

    Shari’ar na nuni da wani muhimmin mataki a ƙoƙarin gwamnati na ƙarfafa ɗaukar alhaki da kuma magance matsalar tsaro da ƙasar ke fama da ita tsawon lokaci.

    Waɗanda ake tuhuma na fuskantar zarge-zarge daban-daban da suka haɗa da kai hare-hare da tallafawa ayyukan ƙugiyoyin masu tsattsauran ra’ayi da ta'addaci.

    Wannan na zuwa ne bayan wata babbar shari’a a watan Afrilun 2026, inda aka gurfanar da sama da mutane 500 kan zargin aikata laifukan ta'addanci kuma an samu kusan 400 da laifi.

    Mahukunta sun ce wannan mataki na da nufin kammala sauran shari’o’i da kuma gurfanar da ƙarin waɗanda ake zargi domin a hukunta su.

    Najeriya na ci gaba da fama da rikicin ta’addanci na tsawon shekaru 16, wanda ya yi sanadin mutuwar dubban mutane tare da raba sama da miliyan biyu da muhallansu, yayin da matsalar garkuwa da mutane ke ci gaba da ƙaruwa a sassa daban-daban na ƙasar.

  8. Farashin mai ya sauka bayan cimma yarjejeniya tsakanin Amurka da Iran

    Farashin hannayen jari ya yi tashin gwauron zabi a kasuwannin Asiya, yayin da farashin mai ya ragu, bayan sanar da cimma yarjejeniya tsakanin Amurka da Iran.

    Farashin ɗanyen man fetur na Brent ya fara sauka da kusan kashi huɗu cikin ɗari, inda ya ragu zuwa ƙasa da dala 84 kan kowace ganga.

    Farashin man ya sakko ƙasa duk da rashin ƙarin bayani kan abun da ke ƙunshe cikin yarjejeniyar, abun da ke nuna yadda 'yan kasuwa suka yi imanin cewa komi zai daidaita da zarar an sake buɗe mashigar Hormuz.

    Kafin rikicin, kusan kashi 20 cikin ɗari na man fetur da iskar gas na duniya na bi ta wannan muhimmiyar hanya da ke yankin Tekun Fasha.

    A lokacin da faɗan ya ɓarke, Iran ta kusan hana zirga-zirgar jiragen ruwa ta wannan mashiga gaba ɗaya.

  9. Rikici ya ɓarke tsakanin ‘yansanda da masu zanga-zanga kafin taron G7 a Turai

    An samu rikici tsakanin ‘yansanda da masu zanga-zanga a dab da fara taron ƙasashen G7, inda suka gwabza a wajen hedkwatar Majalisar Ɗinkin Duniya da ke Geneva, ƙasar Switzerland.

    Rikicin ya faru ne a daidai lokacin da ake shirye-shiryen taron a birnin Évian-les-Bains na Faransa, wanda ke kusa da Geneva, inda biranen biyu ke gefen tafkin Geneva amma a ƙasashe daban-daban.

    An gudanar da zanga-zangar a ranar Lahadi ne karkashin jagorancin wata ƙungiya da ake kira “No-G7”, wadda ta haɗa ƙungiyoyi sama da 60, ciki har da masu fafutukar kare hakkin Falasdinawa da masu rajin kare haƙƙin mata da kuma masu kare muhalli

    Masu zanga-zangar sun jefa kwalabe da duwatsu da kuma gurneti masu ƙara ga jami’an tsaron, yayin da ‘yansandan suka mayar da martani ta hanyar amfani da hayaƙi mai sa hawaye da kuma ruwan zafi wajen tarwatsa su.

    Rahotanni sun ce an kai hari kan wasu gine-gine a yayin rikicin, abin da ya ƙara nuna tashin hankali a yankin.

    Ana sa ran shugabannin ƙasashen G7 da dama za su sauka a filin jirgin saman Geneva kafin su wuce Évian ta cikin tafkin Geneva domin halartar taron.

    Jami’an tsaro na yin shiri ne don tinkarar zanga-zanga makamanciyar wadda aka fuskanta shekaru 23 da suka wuce.

    Haka kuma, babban asibitin birnin ya fara shiri na musamman domin karɓar mutane da ka iya jikkata, inda aka kafa tantuna na wucin gadi domin jinyar gaggawa.

  10. Birtaniya, Faransa, Jamus da Italiya sun yi maraba da yarjejeniyar Iran da Amurka

    Birtaniya, da Faransa, da Jamus da Italiya sun fitar da sanarwar haɗin gwiwa inda suka yi maraba da yarjejeniyar, suna masu cewa sake buɗe mashigar Hormuz abu ne mai matuƙar muhimmanci.

    Sanarwar ta kuma jaddada cewa bai kamata Iran ta taɓa mallakar makamin nukiliya ba.

    Kasashen huɗu na Turai sun ce a shirye suke su ɗage takunkuman da suka sanya wa Iran din idan har ta ɗauki matakai bayyanannu da za su ba da damar bibiyar shirinta na makamashin nukiliya don tabbatar da cewa ba ta sauka daga layi ba.

  11. Iran da Amurka za su rattaɓa hannu kan yarjejeniya ranar Juma'a a Switzerland

    Iran da Amurka sun sanar da cewa sun cimma wata yarjejeniyar fahimtar juna domin kawo ƙarshen yaƙin da ke tsakaninsu, bayan watanni na rikici da tattaunawa.

    Shugaban Amurka, Donald Trump, ya bayyana a wani saƙo cewa yarjejeniya da Iran “ta kammala gaba ɗaya,” yana mai taya kowa murna kan wannan ci gaba.

    Shi ma firaministan Pakistan, Shahbaz Sharif, ya sanar cewa an cimma wannan yarjejeniya, tare da ƙara da cewa za a yi bikin rattaba hannu a hukumance ranar Juma’a, 19 ga watan Yuni, a ƙasar Switzerland.

    Haka zalika, Majalisar Tsaron Ƙasa ta Iran ta tabbatar da cewa an cimma wannan yarjejeniyar fahimtar juna da nufin kawo ƙarshen yaƙin da aka ɗauki watanni ana yi inda ta ce za a dakatar da dukkan ayyukan soja nan take a dukkan wurare.

    Wannan yarjejeniya na daga cikin manyan matakai da ake ganin za su iya rage tashin hankali a yankin Gabas ta Tsakiya tare da buɗe hanya ga zaman lafiya mai ɗorewa.

  12. Assalamu alaikum

    Jama'a barkanmu da wannan safiya ta Litinin daga wannan shafin namu na BBC Hausa, inda za mu ci gaba da kawo muku labaran kai-tsaye na abubuwan da suke faruwa a Najeriya da sassan duniya.

    Aisha Babangida ce ke fatan sake kasancewa da ku a daidai wannan lokaci.

    Za kuma ku iya leƙawa shafukanmu na sada zumunta na facebook da X da kuma whatsapp domin karanta wasu labaran da kallon bidiyo da ma tafka muhawara.

    Ku kasance tare da mu.