Isra'ila tace tana kai hari da iyaka ƙarfinta a kudancin Lebanon
Hukumar Dakarun tsaron Isra'ila ta ba ba da sanarwar mutane sun ƙauracewa yankin kudancin Lebanon inda tace "tana kai hare-harenta na sama a yanzu".
Hukumar tace ana kai harin ne da ƙurewar ƙarfi a yankin kudancin tekun Zahrani, kuma akwai buƙatar mutane su fice daga wajen cikin gaggawa su nufi yankin arewaci.
"Dun wani wanda a yanzu yake zaune a yankin da yake kusa da abubuwan Hezoullah, yana sanya rayuwarsa ne cikin haɗari," kamar yadda sanarwar ta ambato.