Kana amfani da shafin BBC mai bayyana rubutu kawai (babu hoto) domin rage cin data. Idan ana so a ga hotuna da bidiyo sai a koma babban shafinmu.

Koma shafi mai hoto

Samu ƙarin bayani kan shafin tattalin data

KAI TSAYE, Abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya, 14/07/2026

Wannan shafi ne da ke kawo muku labaran abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya, 14/07/2026

Taƙaitattu

  • Dangote ya fara sayar da man fetur da dala
  • An ji ƙarar manyan abubuwan fashewa a Iran
  • Sojojin Jordan sun ce sun kakkaɓo makaman Iran
  • Ƙasashen Gulf za su fara biyan kuɗin tsaron da muke ba su - Trump
  • Iran ta ce ta kai hare-haren kan manyan jiragen dakon mai a mashigar Hormuz

Rahoto kai-tsaye

Abdullahi Bello Diginza

  1. An kai hare-hare a wurare huɗu a birnin Bushehr na Iran

    Mataimakin gwamnan lardin Bushehr mai kula da harkokin tsaro ya ce an kai hare-hare a wurare huɗu da ke cikin birnin Bushehr.

    Ehsan Jahanian ya ce hare-haren sun faru ne da yammacin ranar Litinin agogon ƙasar Iran.

    Ya ce binciken farko da aka gudanar, sun nuna cewa babu rahoton asarar rayuka sakamakon hare-haren.

    Tun da farko kuma, gidan talabijin na ƙasar Iran ya ruwaito cewa an ji ƙarar fashewa har sau biyar a yammacin birnin Bandar Abbas.

    Hare-haren sun faru ne sa'o'i kaɗan bayan Rundunar Sojin Amurka ta CENTCOM ta sanar da kammala wani sabon jerin hare-haren da ta kai kan Iran.

  2. Dangote ya dakatar da sayar da man fetur da naira

    Matatar Dangote ta sanar da dakatar da sayar da mai ga masu sari da kuɗin Najeriya naira.

    A ranar 1 ga watan Oktoban 2024 ne dai Dangote ya fara sayar da mai na naira ga kwastomominsa a Najeriya, bayan cimma wata yarjejeniya da gwamnatin ƙasar, kan wadata ƙasar da man fetur.

    A lokacin an cimma yarjejeniyar cewa gwamnatin Najeriya za ta riƙa sayar masa da ɗanyen mai da naira yayin da shi ma zai riƙa sayar da wanda ya tace da naira.

    Kawo yanzu dai babu wata ƙwaƙƙwarar hujja da Dangoten ya bayar dangane da wannan mataki, to amma wasu jaridun ƙasar na ambato wasu majiyoyi a matatar na cewa a yanzu gwamnati na sayar da matatar ɗanyen mai ne da dala, kuma ba ta sayar mata wanda zai wadace ta.

  3. An ji ƙarar manyan abubuwan fashewa a Iran

    Kafofin yaɗa labaran Iran sun bayar da rahoton jin ƙarar abubuwan fashewa a birnin Bandar Abbas mai gaɓar ruwa, yayin da yaƙi tsakaninta da Iran da Amurka ya tsananta kan iko da mashigar Hormuz.

    Amurka ta ce ta ƙaddamar da hare-hare kan cibiyoyin soji a faɗin Iran cikin dare, domin ruguza ƙarfinta wajen kai wa jiragen ruwa hare-hare.

    A nata ɓangare Iran ta ce ta kai hare-hare kan cibiyoyin sojin Amurka a Bahrain da Jordan, bayan wasu hare-hare da ta kai wa wasu manyan jiragen ruwa a mashigar Hormuz

  4. Sojojin Jordan sun ce sun kakkaɓo makaman Iran

    Rundunar sojin Jordan ta bayyana cewa ta kakkaɓo wasu makaman linzami huɗu da Iran ta harba mana.

    Cikin wata sanarwa da rundunar sojin ta fitar, ta ce dakarun juyin juya halin Iran sun tabbatar da kai hari kan sansanin sojin Amurka da ke Jordan.

    A ƴan kwanakin nan Iran ta riƙa kai hare-hare kan sansanonin sojin Amurka da ƙasashen yankin Gulf, a matsayin martani kan hare-haren da Amurka ta kai mata.

    Ko a safiyar yau Talata sai da rundunar IRGC ta bayyna cewa ta kai hari kan cibiyar sadarwar tauraron ɗan'adam ta Amurka da sansanin sojin Amurka da ke Bahrain.

  5. Ƙasashen Gulf za su fara biyan kuɗin tsaron da muke ba su - Trump

    Shugaban Amurka Donald Trump ya ce dole ne ƙasashen yankin Gulf su biya Amurka saboda kariyar da za ta ba su daga hare-haren Iran.

    Iran ta fara kai hare-hare kan sansanonin sojij Amurka da ke ƙasashen yankin, a matsayin martani kan hare-haren Amurka.

    Yayin da yake magana game da batun a Fadar White House, Shugaba Trump ya ce Amurka za ta ci gaba da bai wa ƙasashen na yankin Gulf tsaro, amma kuma dole ne su biya.

    "Ina so su biya, saboda muna aikin kare yanki mai arziki ne a duniya, don haka ya kamata a biya mu wannan aiki,'' in ji shi.

    Shugaban na Amurka ya ci gaba da cewa ƙasashen na buƙatar taimakon Amurka.

    "Za mu samu kuɗi daga ƙasashe irin su Saudiyya da UAE da Qatar da Bahrain da Kuwait da sauran ƙasashen, Ba mu muke buƙatarsu ba, su ne suke buƙatarmu. Mu muna da wadataccen mai, ciki har da na Venezuela,'' kamar yadda ya yi ƙarin haske.

    Shugaban na Amurka ya kuma bayyana cewa ƙasarsa za ta rufe tasoshin ruwan Iran.

    Ya kuma bayyana cewa za a ɗora wa kowane jirgin dakon mai da zai wuce ta mashigar Hirmzu harajin kashi 20.

  6. Iran ta ce ta kai hare-haren kan manyan jiragen dakon mai a mashigar Hormuz

    Dakarun juyin juya halin Musulunci na Iran sun ce suna kai hare-hare kan manyan tankokin dakon mai a mashigar Hormuz da kuma wuraren da ke da alaƙa da Amurka a ƙasar Bahrain, yayin da rikici a tsakanin Iran da Amurka ke ƙara kamari.

    Dakarun sun ce sun lalata wasu jiragen ruwan dakon mai bayan sun yi watsi da gargaɗin da aka yi musu tare da kashe na’urorin da ke nuna inda suke zirga-zirga.

    A nata ɓangaren, rundunar sojin Amurka ta ce dakarunta sun kai hare-hare kan wuraren da sojoji suke a sassan Iran.

    Rundunar ta kuma ce a yanzu suna da sojoji dubu 50 da aka jibge a yankin Gabas ta Tsakiya.

  7. Assalamu alaikum

    Masu bin shafin BBC Hausa kai-tsaye barkanmu da safiyar wannan rana ta Talata.

    Abdullahi Bello Diginza ke fatan sake kasancewa da ku a daidai wannan lokaci domin kawo muku halin da duniya ke ciki.

    Ku kasance da mu a shafukanmu na sada zumunta domin tafka muhawara kan labaran da muke wallafawa.