Netanyahu ya san wane ne jagora a tsakaninmu - Trump
Shugaban Amurka Donald Trump ya ce firaministan Isra’ila Benjamin Netanyahu ya san wane ne jagora a tasakaninsu yana mai jaddada cewa dangantakar da ke tsakaninsu tana da ƙarfi duk da rahotannin da ke nuna akwai saɓani kan wasu batutuwa.
Trump ya bayyana hakan ne a wata gajeriyar hira da ya yi da kafar Axios, inda ya ce: "Muna da kyakkyawar alaƙa, kuma Netanyahu ya san wane ne jagora."
Kalaman na Trump na zuwa ne yayin da ake sa ran Netanyahu zai kai ziyara Fadar White House nan ba da jimawa ba.
Idan ganawar ta tabbata, za ta kasance ta farko tsakanin shugabannin biyu tun bayan fara yaƙin Iran.
Rahotanni sun nuna cewa akwai saɓanin ra'ayi tsakanin Trump da Netanyahu kan yadda ake tafiyar da wasu batutuwan tsaro, ciki har da yaƙin Iran da kuma matakan da Isra’ila ke ɗauka a Lebanon.