Kana amfani da shafin BBC mai bayyana rubutu kawai (babu hoto) domin rage cin data. Idan ana so a ga hotuna da bidiyo sai a koma babban shafinmu.

Koma shafi mai hoto

Samu ƙarin bayani kan shafin tattalin data

KAI TSAYE, Yaƙin Iran da abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya

Wannan shafi ne da ke kawo muku labarai kan yaƙin Iran da Amurka da Isra'ila da wasu abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya na ranar Talata 09/06/2026.

Rahoto kai-tsaye

Aisha Babangida, Muslim Muhammad Yusuf da Usman MINJIBIR

  1. An ci gaba da yaƙi a Lebanon duk da yarjejeniyar tsagaita wuta

    Isra'ila da Hezbollah a Lebanon sun ci gaba da musayar wuta a tsakaninsu duk da cewa akwai yarjejeniyar tsagaita wuta.

    Kafofin yaɗa labaran Lebanon sun ruwaito cewa aƙalla mutum uku aka kashe a hare-haren Isra'ila a kudancin ƙasar da safiyar yau Talata.

    Wannan na zuwa ne bayan da Iran da Isra'ila suka kai wa junansu hare-hare a karon farko duk da yarjejeniyar tsagaita wuta a watan Afrilu.

    Daga nan ne Isra'ila ta kai hari kan Lebanon, inda ƴan Hezbollah suka mayar da martani.

    Amurka ce ta shiga tsakani wajen tsagaita wutar a ranar 16 ga watan Afrilu, inda duka ɓangarorin ke zargin juna da karya ka'idojin yarjejeniyar.

  2. Ƴan bindiga sun buƙaci miliyan 100 kafin sako dattijan da suka je sulhu a Zamfara

    Ƴan bindigar da suka yi garkuwa da mutum kusan 40 bayan sun tafi yin sulhu da yanfashin daji a ƙaramar hukumar Maradun na Jihar Zamfara sun buƙaci a biya naira miliyan 100 kafin su sako su.

    Mutanen da aka yi garukuwar da su a ranar Lahadi da yamma galibinsu dattawa ne, kamar yadda danmajalisar dokokin jiha mai wakiltar yankin na Maradun Maharazu Salisu ya shaida wa BBC.

    Lamarin ya faru ne a ƙauyen Magamin Diddi wanda rahotanni suka ce yana a kusa da ɗaya daga cikin dazukan da ƴan fashin daji ke da sansani

    A tattaunawarsa da BBC, Sunusi Ahmed Dosara ya ce: "Tun wata uku da suka wuce (ɓarayi) sun hana su (ƙauyen) zaman lafiya, ana cikin haka ne sai ɓarayin suka kwaɗaita musu cewa su zo a yi sulhu domin su bar su, su riƙa cin kasuwa.

    "To daga nan sai dattijai suka je daji domin haɗuwa da ƴan bindiga, amma a lokacin da suka je sai ɓarayin suka riƙe su, sanan suka sako wasu daga cikinsu suka ce ba za su sake su ba sai an cika musu wasu sharuɗaɗa".

    Shugaban ƙaramar hukumar ya ce daga ƙididdigar da suka yi mutanen da ƴan fashin dajin suka riƙe "sun kai 39".

    Ya ƙara da cewa dukkanin mutanen da ake riƙe da su "maza ne dattawa".

  3. Mutum 3 sun mutu a hatsarin jirgin ƙasa a Najeriya

    An tabbatar da mutuwar mutum uku a wani hatsarin jirgin ƙasa a Najeriya, inda kusan mutum 40 suka jikkata.

    Kamar yadda hukumar kula da sufurin jiragen ƙasan Najeriya, NRC ta tabbatar, lamarin ya faru ne a jiya Litnin kuma fasinjoji da dama sun samu raunuka.

    Rahotanni sun ce jirgin ƙasa ya sauka daga kan layinsa ne a hanyar Warri zuwa Itakpe cikin yankin Agbor na jihar Delta a kudancin ƙasar.

    A wata sanarwa da hukumar ta fitar, ta ce tuni ta tura jami'an kai ɗaukin gaggawa da sauran hukumomin da abin ya shafa zuwa wurin da taragan jirgin suka sauka domin ba da taimakon da ya wajaba.

    Sai dai ana fargabar adadin waɗanda suka mutu ya haura uku, kamar yadda wasu ganau suka bayyana.

    Shugaban ƙaramar hukumar Ika North-East Mr. Monday Odigwe, ya shaida wa jaridar Vanguard cewa sama da fasinjoji 35 sun jikkata, inda ake ci gaba da duba su a asibiti.

    Gwamnan jihar Delta Sheriff Oborevwori ya yi jaje ga waɗanda lamarin ya rutsa da su.

    Sufurin jirgin ƙasa a Najeriya ya yi matuƙar taɓarɓarewa, inda ake yawan samun faɗuwar taragai daga kan layin dogo,a wasu hanyoyin ma jiragen kwata-kwata ba sa aiki.

    A ranar 26 ga watan Agustan 2026 ma, wani jirgin ƙasa da ya tashi daga Abuja zuwa Kaduna ya faɗi jim kaɗan bayan barinsa Abuja.

  4. Jirgin Amurka ya faɗo a kusa da Mashigar Hormuz

    Rahotanni sun ce wani jirgin helikwafta na sojin ƙasar Amurka ya faɗo a kusa da Mashigar Hormuz.

    Jaridar New York Times ta ruwaito cewa "wasu majiyoyi" biyu sun shaida mata cewa jirgin ya faɗo ne a jiya Litinin, kuma a ceto duka mutane biyu da ke cikin jirgin.

    Sai dai ba a tabbatar ko dakarun Iran ne suka harbo jirgin ba, ko kuma ya samu tangarɗar na'ura ne.

    Shugabanm Amurka Donald Trump ya sanar da cewa duka matuƙan jirgin "suna cikin ƙoshin lafiya"

    "Babu wanda ya ji rauni," in ji Trump.

    Ya ƙara da cewa gwamnati za ta saki cikakken rahoto game da lamarin a yau Talata.

  5. Netanyahu bai yi biris da umarni na ba - Trump

    Shugaban Amurka Donald Trump ya jaddada cewa firaministan Isra’ila bai yi biris da umarninsa ba, na dakatar da kai hari kan Iran a ranar Litinin.

    Da yake magana da BBC, Trump ya ce sai da aka harba makamai masu linzamin sannan ya shaidawa Benjamin Netanyahu kada ya mayar da martani ga hare-haren Tehran.

    A yanzu dai Iran da Isra’ila sun dakatar da kai wa juna hare-hare, to amma sun yi gargadin cewa za su iya komawa faɗan idan lamarin ya sake taɓarɓarewa.

    Tehran dai ta yi barazanar daukar ƙwararan matakai a kan Isra'ila idan har aka ci da kai hare hare a Lebanon, inda sojojin Isra'ila ke faɗa da ƴan Hezbollah.

    A ranar Lahadi ne Isra'ila ta kai hari kan wurin da Hezbollah ke da karfi a kudancin Beirut, inda su ma ƴan Hezbollah suka mayar da martani ta hanyar harba makaman roka.

  6. Assalamu Alaikum!

    Barka da zuwa shafin BBC Hausa na kai-tsaye.

    Kamar kullum, yau ma za mu muku labaran abubuwan da ke faruwa game da yaƙin Iran da wasu muhimman abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya a wannan rana ta Talata.

    Za ku iya yin tsokaci a shafukanmu na sada zumunta: Facebook, X, instagram, YouTube da kuma zaurenmu na WhatssApp.