An ci gaba da yaƙi a Lebanon duk da yarjejeniyar tsagaita wuta
Isra'ila da Hezbollah a Lebanon sun ci gaba da musayar wuta a tsakaninsu duk da cewa akwai yarjejeniyar tsagaita wuta.
Kafofin yaɗa labaran Lebanon sun ruwaito cewa aƙalla mutum uku aka kashe a hare-haren Isra'ila a kudancin ƙasar da safiyar yau Talata.
Wannan na zuwa ne bayan da Iran da Isra'ila suka kai wa junansu hare-hare a karon farko duk da yarjejeniyar tsagaita wuta a watan Afrilu.
Daga nan ne Isra'ila ta kai hari kan Lebanon, inda ƴan Hezbollah suka mayar da martani.
Amurka ce ta shiga tsakani wajen tsagaita wutar a ranar 16 ga watan Afrilu, inda duka ɓangarorin ke zargin juna da karya ka'idojin yarjejeniyar.