Rahotonni daga jihar Zamfara da ke arewa maso yammacin Najeriya sun bayyana cewa jami'an tsaron ƙasar sun yi nasarar kashe wasu manyan barayin daji 65 .
Bayanai sun ce daga cikin waɗanda aka kashe har da ƴaƴan ƙasurgumin ɗanfashin daji Ado Aleiru uku waɗanda suka addabi yankin Tsafe.
Mannir Sani Fura Girke ɗanjarida ne mai binciken ayyukan ƴanbindiga a arewa maso yammcin Najeriya ya kuma shaida wa BBC cewa lamarin ya faru ne lokacin da ƴanbindigar, ƙarƙashin jagorancin Ado Aleiro suka yi yunƙurin kai hari kan sabon sansanin jami'an tsaro da aka buɗe a garin ƙunshin Kalgo, inda kuma jami'an tsaron suka mayar da martani.
''Tun maraicen ranar Asabar ɓangarorin biyu suke musayar wuta tsakaninsu har zuwa wayewar garin Lahadi ake fafatawa'', in ji shi.
Ya ci gaba da cewa fafatawar ta yi sanadin kisan ƴanbindigar kusan 65, ciki har da ƴaƴan Ado Aleiro.
''Daga ciki akwai ƴaƴan Ado Aliero na cikinsa har guda uku, ciki har da babban ɗansa, Sarki da Ahmadu da Iliya, duka ƴaƴansa ne na cikinsa, kuma an kashe su'', in ji ɗanjaridar.
Mannir Girke ya ce baya da ƴaƴan Ado Aliero an kuma kashe manƴan kwamandojin tawagar tasa da suka haɗa da Kacalla Hukuma da Kacalla Dogo Burti da Kacalla Baƙin Sifindi da Kacalla Mani Mugu da Kacalla Iliya mai Rasha.
''Duka waɗannan su ne manyan jagororin tawagar da suka jagoranci wannan faɗan'', kamar yadda ya yi ƙarin haske.
Mai bincike kan ayyukan ƴanfashin dajin ya ce ba a jima da buɗe sabon sansanin sojin a garin Ƙuncin Kalgo, wanda ke kusa da dajin Munhaye, da ya yi ƙaurin suna a matsayin mafakar ƴanbindiga.
''Duk ɓarayin da suka fito daga dajin Munhaye ta Ƙuncin Kalgo suke bi domin su je yammacin tsafe, ko su bu hanyar Gusau ko su je Faskari ko su shiga yankuna Bakori da Kankara'', in ji shi.
Ya ce girka jami'an tsaro a wannan sabon sansanin ba ƙaramar nasara ba ce ga rundunar sojin Najeriya, musamman a wannan muri mai matuƙar muhimmanci ga ayyukan ƴanbindigar.